• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

by Yusuf Shuaibu
2 hours ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar dattawa ta bayyana cewa majalisar tarayya za ta duba dukkan muhimman abubuwan da suka dace kafin ta ba da shawarar da amincewa da kowanne bukata na kirkirar sabbin jihohi a duk fadin kasar.

Majalisar dattawan ta jaddada cewa, duk da dai wasu ‘yan Nijeriya na nema a kirkiro karin sabbin jihohi, za a kula da batun tare da gudanar da cikakken nazari tare da batun son kai ko bukatu na kashin kai ba.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Mai magana da yawun majalisar dattawa kuma shugaban kwamitin harkokin kafafen yada labarai, Sanata Yemi Adaramodu, ya bayyana hakan a karshen mako yayin da yake magana da manema labarai a gidansa da ke Ilawe-Ekiti cikin Jihar Ekiti. Ya bayyana cewa an riga an karbi kudirin bukatun kirkirar sabbin jihohi har guda 61.

Sanatan, wanda ke wakiltar Yankin mazabar Ekiti ta Kudu, ya tabbatar da cewa za a bi hanyoyin da suka dace kafin a gabatar da kowanne kudiri.

Ya ce, “Zuwa yanzu dai, majalisar dattawa ta karbi kusan kudirorin bukatun kirkirar sabbin jihohi har guda 61. A cikin tattaunawarmu a lokacin sauraren jin ra’ayoyin jama’a a dukkan fadin kasar nan, an dai gabatar da wadannan bukatu a hukumance. Kamar yadda muka bayyana, dukkansu za a duba su da kuma yin kyakkyawan Nazari a kansu.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

“Mun amshe bukatun, sannan bayan hakan kwamitin yin nazari kan sake yi wa tsarin mulki garambawul wanda mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Jibrin Barau yake jagoranta zai tattance tare da shirya rahoto ga majalisar.

“Da zarar rahoton ya kammala, majalisar dattawa tare da hadin gwiwar majalisar wakilai za su gudanar da cikakken jin ra’ayin jama’a. Wannan zai ba da dama ga dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da masu goyon baya da masu adawa su gabatar da hujjojinsu. Bayan haka, majalisun guda biyu za su yanke shawara kan wadannan bukatun.

“Batun kirkirar sabbin jihohi abu ne mai matukar muhimmanci wanda ke bukatar duba batutuwan al’umma, yankuna, da samun alkaluman tarihi. A wasu lokuta, ko a cikin jihohin da suka nema, ba a samu cikakken yarda ba. Dukkan wadannan abubuwan dole ne a yi la’akari da su. Kafin wannan, majalisaun tarayya ba su da hurumin amincewa da kirkirar wata sabuwar jiha.

“Kamar yadda ake ciki a halin yanzu, babu jihar da aka ba da shawara a kirkira. Ba za mu iya tabbatar da rahotanni na karshe ba ko zartar da hukunci kan jin ra’ayin jama’a da aka hada ba har sai an kammala sauraron jin ra’ayin jama’a gaba daya zuwa lokacin da muka dawo,” in ji shi.

Ya jaddada cewa ‘yan majalisar za su ba da muhimmanci ga sha’anin kasa sama da ra’ayoyinsu a yayin yanke shawarar kan batun yin garambawu a kundin tsarin mulkin kasar nan.

“Majalisar tarayya dai wuri ne na yin dokoki da kuma kula da aikin tsarawa ko gyara kundin tsarin mulki. Muna kira ga ’yan’uwanmu ‘yan majalisa su yi amfani da wannan dama da za ta dace ga kowa da kowa.

“Muna maraba da shawarwari daga dukkan ‘yan Nijeriya da suka hada da dattawa da kwararru da shugabannin siyasa da sarakunan gargajiya da kungiyoyin matasa da kungiyoyin mata da kungiyoyin farar hula, har ma da ‘yan Nijeriya da ke zaune a kasashen waje.

“Za a bude taron sauraron jin ra’ayoyin jama’a ga kowa, kuma kundin na karshe kan gyara tsarin mulkin kasar nan zai bayyana batutuwan da ‘yan Nijeriya suka yanke hukunci a kai, ba ra’ayin wata kungiya kadai ba.

“Manufarmu ita ce, tabbatar da duk wasu canje-canje da za a yi a kundin tsarin mulki su kasance mafi kyawu ga bukatar Nijeriya da kuma mutanenta,” in ji Adaramodu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jihohi
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

Next Post

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Related

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 hour ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

3 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

3 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

4 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 weeks ago
Next Post
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.