ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Samu Damar Karɓar Baƙuncin Taron Hulɗa Da Jama’a Na Duniya Na 2026

by Sulaiman
1 year ago
Nijeriya

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya taya Ƙungiyar Masana Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (NIPR) murna kan samun damar karɓar baƙuncin Taron Hulɗa da Jama’a na Duniya (World Public Relations Forum, WPRF) na shekarar 2026.

 

Sanarwar ta zo ne yayin wata ziyarar girmamawa da Shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, da tawagar sa suka kai wa ministan a ranar 6 ga Maris, 2025.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Naɗa Jega Muƙamin Mai Ba Shi Shawara Kan Harkar Kiwo
  • Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliyoyin Naira Kan Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba – Gwamnati

Ministan ya jaddada muhimmancin taron WPRF, wanda ke haɗa shugabanni da masana a fannin hulɗa da jama’a da sadarwa.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

Ya bayyana cewa samun damar karɓar baƙuncin wannan babban taro wata gagarumar nasara ce ga Nijeriya, kasancewar ita ce ƙasar Afirka ta biyu da za ta karɓi baƙuncin taron.

 

Ya ce: “Wannan babban cigaba ne ga Nijeriya kuma yana da alaƙa da manufofin gwamnatin mu na inganta martabar ƙasar a idon duniya. A daidai lokacin da muke aiwatar da muhimman sauye-sauye da ƙarfafa matsayar mu a duniya, karɓar baƙuncin WPRF wata alama ce cewa duniya tana kallon Nijeriya.

 

“Gwamnati za ta bayar da cikakken goyon baya don tabbatar da nasarar wannan taro.”

 

Ya kuma bayyana wata muhimmiyar nasara, inda ya ce Nijeriya ta samu damar karɓar baƙuncin Cibiyar UNESCO ta Mataki na Biyu kan Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Bayani (MIL), wadda ita ce irin ta ta farko a Afrika.

 

Ya ce wannan matakin yana nuna irin girman tasirin da Nijeriya take samu a duniya.

 

Ya ce: “Hulɗa da jama’a tana da muhimmiyar rawa wajen gina ƙasa, bunƙasa dimokiraɗiyya, da inganta martabar Nijeriya a duniya.

 

“Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai tana da ecikakken niyyar yin aiki tare da duk masu ruwa da tsaki domin cimma wannan buri da kuma ba Nijeriya matsayi na jagora a fagen sadarwa na duniya.”

 

A nasa jawabin, Shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, ya yaba wa ministan bisa ƙwazon da yake yi wajen inganta sarrafa bayanai da hulɗa da jama’a a ƙasar.

 

Ya ce: “Yanzu muna kallon sarrafa bayanai a matsayin hanyar sadarwa ta ɓangarori biyu, wato inda muke karɓar ra’ayoyi daga jama’a don su taimaka mana wajen tsara matakai na gaba.”

 

Dakta Neliaku ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta karɓi baƙuncin bikin cika shekaru 25 na ƙungiyar Global Alliance a shekarar 2026, wanda hakan zai ƙara tabbatar da matsayin ƙasar a matsayin jagaba a fagen hulɗa da jama’a a duniya.

 

Bugu da ƙari, ya sanar da ministan manyan shirye-shiryen da NIPR ta tsara na shekarar 2025, wanda suka haɗa da Makon Hulɗa da Jama’a na Nijeriya (NPR Week), Taron Ƙasa na Masu Magana da Yawu, da Taron Ƙasa kan Sarrafa Sunan Nijeriya.

 

Tawagar shugabannin NIPR ɗin ta haɗa da Mataimakin Shugaba, Farfesa Emmanuel Dandaura, da wasu manyan jami’ai, ciki har da Cif Yomi Badejo-Okusanya, Mohammed Kudu Abubakar, da Cif Uzoma Onyegbadue.

Nijeriya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
Labarai

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Next Post
Babban Darektan Jaridar The Guardian Ta Tanzaniya: Abubuwan Da Aka Tattauna a Manyan Taruka Biyu Na Sin Na Da Alaka Da Kasashen Duniya

Babban Darektan Jaridar The Guardian Ta Tanzaniya: Abubuwan Da Aka Tattauna a Manyan Taruka Biyu Na Sin Na Da Alaka Da Kasashen Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.