Tsohon shugaban Ƙungiyar Tuntuɓa Kan Gamayyar Jam’iyyun Siyasa na Kasa (IPAC), Peter Ameh, ya soki hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta yanke kan rajistar jam’iyyar NDC, yana mai cewa hukuncin “barazana ce ga dimokuraɗiyya da kuma mulkin doka.”
Ameh, wanda kuma yake riƙe da muƙamin shugaban riƙo na Ƙungiyar Gamayyar Jam’iyyun Siyasa (CUPP), ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Abuja.
Ya ce hukuncin kotun, wanda a cewarsa ya sake duba wani hukunci ne na baya da ya amince da rajistar NDC, ya haifar da damuwa game da ‘yancin kai na ɓangaren shari’a, ƙarfin hukuncin kotu na ƙarshe da kuma sahihancin tsarin shari’ar Nijeriya.
A cewarsa, “abin dariya ne kotu ta amince da soke rajistar jam’iyyar siyasa da aka yi wa rijista bisa ƙa’ida, saboda kawai wata ƙungiya da ba a yi wa rajista ba kuma ba ta da matsayi a doka ta nemi yin hakan.”
Kalaman Ameh na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama kan matsayin doka da shugabancin wasu jam’iyyun siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027.














