Gwamnatin Jihar Oyo ta sanya dokar hana fita a ƙananan hukumomi 10 da ke kewaye da dajin ajiye dabbobi na ƙasa na “Old Oyo National Park”, a matsayin ɓangare na ƙoƙarin tunkurar ayyukan garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka a yankin.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar, Dotun Oyelade ya fitar, gwamnatin ta ce dokar hana fitar za ta fara aiki ne daga ƙarfe 4:00 na yamma zuwa ƙarfe 8:00 na safe na kowace rana, tun daga ranar Laraba, 24 ga watan Yuni, 2026.
Wannan takunkumi zai ci gaba da aiki na tsawon sa’o’i 48 a matakin farko.
Ƙananan hukumomin da wannan doka ta shafa sun haƊa da: Oriire, Orelope, Irepo, Saki West, Saki East, Atisbo, Itesiwaju, Iseyin, Olorunsogo, da Atiba.
Oyelade ya bayyana cewa an Ɗauki wannan mataki ne domin bayar da goyon baya ga ayyukan tsaro da ake gudanarwa a halin yanzu da kuma dawo da zaman lafiya a yankunan da ke maƙwabtaka da dajin na ƙasa.
Ya buƙaci mazauna yankunan da su bi wannan umurni, a daidai lokacin da hukumomin tsaro ke tsananta ƙoƙarinsu na kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
Dalilin daukar wannan mataki
Wannan dokar hana fita ta biyo bayan wasu abubuwan ban tsoro na sace mutane da yawa da suka faru a yankin Oriire kwanan nan.
A watan Mayun 2026, wasu ƴan bindiga sun kai hari makarantu a yankunan Yawota da Ahoro-Esinle, inda suka yi garkuwa da gomman ɗalibai da malamai, sannan suka kashe a ƙalla malami guda ɗaya.
A cewar gwamnatin jihar, an yi awon gaba da mutumn ne zuwa cikin dajin “Old Oyo National Park”, wani babban daji mai faɗin gaske wanda a yanzu yake ci gaba da zama maɓoyar ƙungiyoyin ƴan bindiga.
A halin yanzu, hukumomin tsaro suna gudanar da ayyukan bincike da ceto a cikin yankin.













