Iran ta sake jaddada cewa ba za ta ba Hukumar Kula da Makaman Nukiliya ta Duniya (IAEA) damar binciken wasu wuraren nukiliyarta da suka lalace ba.
Mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar, Kazem Gharibabadi, ya ce ba a yi wata ganawa tsakaninsa da shugaban IAEA, Rafael Grossi, a Switzerland ba, duk da roƙon da aka gabatar.
Ya kuma ƙara da cewa babu wani shiri na buɗe wuraren da aka kai wa hari ga masu bincike na hukumar.
Wannan matsayi na Iran ya zo ne bayan shugaban IAEA ya bayyana cewa ana sa ran sake fara bincike a wuraren nukiliyar ƙasa
Rafael Grossi ya shaida wa manema labarai a Japan cewa yarjejeniyar tsakanin Amurka da Iran ta tanadi cewa ayyukan nukiliya za su kasance ƙarƙashin sa ido na hukumar, yana mai jaddada cewa dole ne a gudanar da bincike, ko da yake ba a ƙayyade lokacin da hakan zai faru ba.
Sai dai Iran ta musanta hakan, tana mai cewa babu wata sabuwar yarjejeniya da ta ɗauka kan batun nukiliya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, Esmail Baghaei, ya ce babu doka da ta tilasta wa Iran ba da damar binciken wuraren da hare-haren soji suka lalata.
A gefe guda, shugaban Amurka Donald Trump da mataimakinsa JD Ɓance sun ce Iran ta amince da sa mata ido na dogon lokaci kan shirinta na nukiliya, iƙirarin da gwamnatin Tehran ta ƙaryata.














