Gwamnatin Ghana ta soke duk wani lasisin mallakar bindigogin da aka bai wa fararen hula matakin da ya fara aiki nan take, tare da ƙaddamar da wani tsari mai tsauri na tantance masu neman lasisin.
Yayin jawabin sa a wani taron manema labarai Ministan harkokin cikin gida na ƙasar Muntaka Mohammed Mubarak ya ce, matakin ya biyo bayan yadda ake ganganci wajen amfani da wasu makaman yana mai cewa matakin zai taimaka wajen kariya kan matsalolin da za su haifar a nan gaba.
Ministan ya sanar da soke lasisin makamai fiye da 2,000 da aka karɓe, a ƙoƙarin tsaurara dokokin sarrafa makamai, da rage waɗanda basu da rijista.
Minintan ya ƙara da cewa, a ƙarƙashin sabon tsarin, masu neman lasisin zasu sake yin rajista tare da fuskantar gwajin lafiyar ƙwaƙwalwa, gwajin miyagun ƙwayoyi da kuma horaswa kan amfani da makamai.
Gwamnati ta ɗauki matakin soke lasisin ne bayan da dakatar da wasu kamfanonin tsaro masu zaman kansu da ake zargi da yin amfani da kakin jami’an tsaro tare da mallakar makamai da alburusai ba a kan ƙa’ida ba.
Daga bisani gwamnatin ta Ghana ta sanar da cewa zata buɗe wani sabon tsarin rijista domin bai wa masu makamai damar sake neman lasisi bisa sabbin ƙa’i’dojin da aka tanada.














