• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayi: Jama’a A Yi Rajistar Zabe Domin Kar Mata Ta Kada Miji

bySulaiman
3 years ago
katin zabe

Ina kira ga daukacin ‘yan kasar nan a kowane sashi suke su yi rajistar zabe saboda kalubalen da ke tattare da zabe mai zuwa. Ga dalilaina guda uku na yin wanna kira.

Ambaliya
Sakamakon zaben fid da gwani na ‘yan takarar shugaban kasa ya kawo ambaliyar masu rajistar jefa kuri’a, musamman a yankunan Inyamurai da Yarbawa.

  • Wainar Da Aka Toya A Zaben Dan Takarar APC Na Shugaban Kasa

Dafifin mutanen ba karami ba ne, domin ya sa har hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta kara na’urorin rajista a jihohi biyar a yankunan Inyamurai da Jihar Legas da kuma Jihar Kano. 5-1-1. Me wannan lissafin ya nuna maka? Kuma me ya jawo wannan dafifi?
Ina ga ba zai rasa nasaba da kokarin da kowane sashi yake yi ba don ya taimaka wa nasa dan takarar da kuri’u masu yawa, don idan kowanne zai samu daukacin masu jefa kuri’a a sashinsa, ba shakka likkafarsa za ta ja gaba.

A nan, ‘yan arewa suna da matsalar ko-oho (complacency) ganin cewa suna da yawa. Ina ga wannan babban kusukure ne. Jefa kuri’a a yau ya zama wajibi ga duk wanda yake son ya ga an samu ci gaba a kan abin da ya dame shi. Yau muna cikin tasku na rashin zaman lafiya.

Ya kamata a ce mun fi kowa damuwa da waye zai zama shugaban kasa, saboda shi ne zai shugabanci hukumomin tsaro gaba daya. Idan wani zai yi amfani da su ya taimake mu, wani zai iya amfani da su ya cutar da mu.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

In mun yi watsi da zabe mai zuwa, yana yiyuwa abubuwa su kara tabarbarewa har inda fitinar ba ta kai ba yau ta kai a gobe, ko a bullo da wasu sababbin fitinu. Su ma sauran sassan kasar suna da abubuwan da ke damunsu kuma a kan haka za su jefa kuri’a. To me zai sa ba za mu himmatu ba kamar yadda suke nuna himma a kwanakin nan?

Tuwon Gobe
Na yarda akwai mutane da yawa da rashin kyan mulkin Buhari ya kashe wa gwiwa. Ga mai hankali, wannan shi ne ma zai sa a kara himma, a gwada wani watakila a yi dace, domin ana zaton wuta a makera a same ta a masaka. Ala ayyi halin, mu ‘yan kasa mu yi namu. Mu zaba. Idan wadanda muka zaba suka ci amanarmu ko suka gaza, sai mu bar su da Allah. Rashin dadin tuwon yau ba shi zai hana mu cin na gobe ba.

Ingancin Zabe
Bugu da kari, yau kuri’a tana da muhimmanci ba kamar a baya ba, don an ci karfin magudi a lokacin zabe. Wannan ci gaba ya samu ne don rajistar masu jefa kuri’a da aka samar tun zamanin marigayi Yar’adua (Allah ya masa rahama), da amfani da fasahohin zamani na tantance masu jefa kuri’a, da aikawa da sakamako daga mazabu kai-tsaye zuwa rumbun bayanai na INEC, da kuma uwa-uba dokoki daban-dabam da ke cikin dokokin zabe da aka kafa tun 2011.

Yau idan mutum ya jefa kuri’a akwai tabbaci mai rinjaye cewa za a kirga ta a yawan kuri’un dan takarar da ya jefawa. Me ya fi haka dadi? Ba a gama seta komi da komi ba, amma dai an ci karfin magudi. Wanda aka tafka a shekarun baya ba za a sake iya yin sa ba a yanzu. Don haka wadanda da suke cewa kuri’arsu ba ta da amfani, ya kamata su bar wannan turbar, su fara yin zabe.

Sakiyar Da Ba Ruwa
Don wadannan dalilai, ina kira ga kowa ya tsaya kan wadanda yake da iko a kansu ko wadanda suke jin maganarsa ya tabbatar da kowannensu ya yi rajista. Kuma idan lokacin zabe ya zo, kowa ya jefa kuri’arsa ga wanda ya fi zaton zai fi alheri da kawo ci gaba a kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Zaben Fitar Da Gwani: Tsarin Daliget Ya Yi Kancal Ga Yawancin ‘Yan Majalisarmu —Gbajabiamila

Zaben Fitar Da Gwani: Tsarin Daliget Ya Yi Kancal Ga Yawancin ‘Yan Majalisarmu —Gbajabiamila

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version