ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayi: Jama’a A Yi Rajistar Zabe Domin Kar Mata Ta Kada Miji

by Sulaiman
4 years ago
katin zabe

Ina kira ga daukacin ‘yan kasar nan a kowane sashi suke su yi rajistar zabe saboda kalubalen da ke tattare da zabe mai zuwa. Ga dalilaina guda uku na yin wanna kira.

Ambaliya
Sakamakon zaben fid da gwani na ‘yan takarar shugaban kasa ya kawo ambaliyar masu rajistar jefa kuri’a, musamman a yankunan Inyamurai da Yarbawa.

  • Wainar Da Aka Toya A Zaben Dan Takarar APC Na Shugaban Kasa

Dafifin mutanen ba karami ba ne, domin ya sa har hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta kara na’urorin rajista a jihohi biyar a yankunan Inyamurai da Jihar Legas da kuma Jihar Kano. 5-1-1. Me wannan lissafin ya nuna maka? Kuma me ya jawo wannan dafifi?
Ina ga ba zai rasa nasaba da kokarin da kowane sashi yake yi ba don ya taimaka wa nasa dan takarar da kuri’u masu yawa, don idan kowanne zai samu daukacin masu jefa kuri’a a sashinsa, ba shakka likkafarsa za ta ja gaba.

ADVERTISEMENT

A nan, ‘yan arewa suna da matsalar ko-oho (complacency) ganin cewa suna da yawa. Ina ga wannan babban kusukure ne. Jefa kuri’a a yau ya zama wajibi ga duk wanda yake son ya ga an samu ci gaba a kan abin da ya dame shi. Yau muna cikin tasku na rashin zaman lafiya.

Ya kamata a ce mun fi kowa damuwa da waye zai zama shugaban kasa, saboda shi ne zai shugabanci hukumomin tsaro gaba daya. Idan wani zai yi amfani da su ya taimake mu, wani zai iya amfani da su ya cutar da mu.

LABARAI MASU NASABA

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

In mun yi watsi da zabe mai zuwa, yana yiyuwa abubuwa su kara tabarbarewa har inda fitinar ba ta kai ba yau ta kai a gobe, ko a bullo da wasu sababbin fitinu. Su ma sauran sassan kasar suna da abubuwan da ke damunsu kuma a kan haka za su jefa kuri’a. To me zai sa ba za mu himmatu ba kamar yadda suke nuna himma a kwanakin nan?

Tuwon Gobe
Na yarda akwai mutane da yawa da rashin kyan mulkin Buhari ya kashe wa gwiwa. Ga mai hankali, wannan shi ne ma zai sa a kara himma, a gwada wani watakila a yi dace, domin ana zaton wuta a makera a same ta a masaka. Ala ayyi halin, mu ‘yan kasa mu yi namu. Mu zaba. Idan wadanda muka zaba suka ci amanarmu ko suka gaza, sai mu bar su da Allah. Rashin dadin tuwon yau ba shi zai hana mu cin na gobe ba.

Ingancin Zabe
Bugu da kari, yau kuri’a tana da muhimmanci ba kamar a baya ba, don an ci karfin magudi a lokacin zabe. Wannan ci gaba ya samu ne don rajistar masu jefa kuri’a da aka samar tun zamanin marigayi Yar’adua (Allah ya masa rahama), da amfani da fasahohin zamani na tantance masu jefa kuri’a, da aikawa da sakamako daga mazabu kai-tsaye zuwa rumbun bayanai na INEC, da kuma uwa-uba dokoki daban-dabam da ke cikin dokokin zabe da aka kafa tun 2011.

Yau idan mutum ya jefa kuri’a akwai tabbaci mai rinjaye cewa za a kirga ta a yawan kuri’un dan takarar da ya jefawa. Me ya fi haka dadi? Ba a gama seta komi da komi ba, amma dai an ci karfin magudi. Wanda aka tafka a shekarun baya ba za a sake iya yin sa ba a yanzu. Don haka wadanda da suke cewa kuri’arsu ba ta da amfani, ya kamata su bar wannan turbar, su fara yin zabe.

Sakiyar Da Ba Ruwa
Don wadannan dalilai, ina kira ga kowa ya tsaya kan wadanda yake da iko a kansu ko wadanda suke jin maganarsa ya tabbatar da kowannensu ya yi rajista. Kuma idan lokacin zabe ya zo, kowa ya jefa kuri’arsa ga wanda ya fi zaton zai fi alheri da kawo ci gaba a kasa.

Zabe
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • Sulaiman
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

MASU ALAKA

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
Tambarin Dimokuradiyya

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Next Post
Zaben Fitar Da Gwani: Tsarin Daliget Ya Yi Kancal Ga Yawancin ‘Yan Majalisarmu —Gbajabiamila

Zaben Fitar Da Gwani: Tsarin Daliget Ya Yi Kancal Ga Yawancin ‘Yan Majalisarmu —Gbajabiamila

LABARAI MASU NASABA

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.