Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ƙaddamar da wani shirin inganta tsaron abinci na dala miliyan 1, tare da sanar da tallafin kuɗi har Naira miliyan 1 ga matasa masu harkar noma da mata domin ƙarfafa samar da abinci da inganta rayuwar al’umma.
Shirin mai taken “Kare Tsaron Abinci Daga Ambaliyar Ruwa Da Fari”, ƙungiyar Mercy Corps Nigeria ce za ta aiwatar tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Ci gaban Jihar Katsina da Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki.
Gwamna Radda ya ce shirin na tsawon watanni 12 zai fara ne a ƙananan hukumomin Bindawa, Bakori da Kafur, domin taimaka wa manoma wajen fuskantar matsalolin sauyin yanayi.
Ya ce za a gyara rijiyoyin ruwa masu amfani da hasken rana guda 12, inganta gonaki 150, farfaɗo da filayen da suka lalace, gyara rumbunan ajiyar abinci 150, tare da raba buhunan adana hatsi guda 500.
Shirin zai kuma tallafa wa noman da ya dace da sauyin yanayi, samar da wasu hanyoyin samun kuɗin shiga ga mata kusan 300, da kuma ayyukan samun kuɗi kai tsaye ga mutane 180.
A wani ɓangare, Radda ya sanar da tallafin fara sana’a na Naira miliyan 1 ga kowane ɗaya daga cikin matasa 361 da suka kammala zangon biyu na shirin koyar da noma na DRATESS-Songhai.
Ya ce kowanne daga cikin waɗanda suka amfana zai fara da N500,000, yayin da za a sakin sauran kuɗin a matakai bisa yadda suka kafa sana’o’insu da kuma yadda suke gudanar da su.
Gwamnan ya kuma ce za a faɗaɗa cibiyar Makera Songhai domin ta riƙa ɗaukar mutane har 1,000, yana kira ga waɗanda suka kammala horon da su mayar da ilimin zuwa sana’o’i tare da samar da ayyukan yi.
Haka kuma, Radda ya duba wata motar gyara ta tafi-da-gidanka da aka saya domin gyara da kula da taraktocin jihar guda 400 a yankunan manoma.
Majalisar Zartarwar Jihar ta kuma amince da shirin tallafa wa mata 49,640 a unguwanni 361 da ƙananan hukumomi 34, tare da amincewa da aikin sake gina hanyar Bindawa–Dallaje–Doro–Giremawa–Duwan zuwa mahaɗar Duwan.













