Gwamnatin Jihar Bauchi ta yi Allah-wadai da kama wasu masu kaɗa ƙuri’a yayin zaɓen cike gurbin kujerun majalisar dokokin jihar da aka gudanar ranar Asabar.
Mataimakin Gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau, ya buƙaci hukumomin tsaro da su gaggauta sakin mutanen da aka kama a mazaɓun Sakwa da Disina, da ke ƙananan hukumomin Zaki da Shira.
Jatau ya ce kama masu kaɗa ƙuri’a tare da hana su yin amfani da haƙƙinsu na zaɓe abin damuwa ne, yana mai kira ga hukumomin tsaro da su tabbatar da zaman lafiya da bin doka.
Ya kuma zargi wasu jami’an tsaro da aka turo daga Abuja da kama wasu magoya bayan jam’iyyar APM, yana cewa bai kamata a tsare su ba idan ba a same su da laifi ba.
Sai dai rundunar ’yansandan Bauchi ta ce mutanen da ta kama 50 ’yan wata ƙungiyar tsaro ce ta sa-kai da gwamnatin jihar ta kafa, kuma an same su a rumfunan zaɓe ɗauke da makamai.
’Yansandan sun ce irin waɗannan ƙungiyoyi ba su da izinin shiga aikin tsaro a rumfunan zaɓe.














