Wani Babban Lauyan Nijeriya (SAN), Shaibu Enejo Aruwa, ya rubuta wa Babbar Mai Shari’ar ta Kasa, Kudirat Kekere-Ekun (CJN), yana roƙon Kotun Ƙoli da ta gaggauta yanke hukunci kan ɗaukaka ƙarar da ke gaban kotu dangane da rikicin shugabancin Jam’iyyar ADC tsakanin tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, da Nafiu Bala Gombe.
Lauyan ya yi gargadin cewa jinkirin yanke hukuncin na iya kawo cikas ga shirin jam’iyyar na shiga zaɓen 2027.
A cikin wasiƙar da aka rubuta ranar Talata, 28 ga Afrilu, 2026, Aruwa, wanda lauya ne ga ADC, ya buƙaci a tabbatar da “gaggauta yanke hukunci” a shari’ar mai lamba SC/CV/180/2026.Jaridar LEADERSHIP ta tuna cewa an saurari ƙarar mai taken “Sanata David Mark da Hon. Nafiu Bala Gombe da wasu mutum 4” a ranar 22 ga Afrilu, 2026, inda kotu ta ajiye hukunci zuwa wani lokaci na gaba.
Aruwa ya bayyana damuwa cewa jinkirin yanke hukuncin na iya haifar da babbar matsala ga makomar siyasar jam’iyyar, musamman duba da matakan da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ɗauka kwanan nan.
“Cikin girmamawa muke roƙon mai girma CJN da ta sa baki domin tabbatar da cewa an yanke hukuncin cikin lokaci,” in ji wasiƙar.
Ya kuma bayyana cewa INEC, bisa wani hukuncin ƙaramar kotu a ƙarar mai lamba CA/ABJ/145/2026, ta “cire ko ta daina amincewa da shugabancin ADC,” lamarin da ya bar jam’iyyar ba tare da ingantaccen tsarin shugabanci ba.
A cewarsa, duk da cewa ADC har yanzu jam’iyya ce mai rijista, rashin shugabanci na iya hana ta cika wasu muhimman sharudda da INEC ta tsara domin zaɓen 2027.















Discussion about this post