• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharuddan Da ACF Ke Son Duk Mai Neman Ya Gaji Ganduje Ya Cika

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Hanya Mafi Sauki Ta Magance Matsalolin Sashin Shari’a – Ganduje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa ta ACF reshen Jihar Kano ta gindaya sharudda ga dukkan ‘yan takarar gwamna da ke jam’iyyu daban-daban wadanda suke son gadar Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a 2023.

Shugaban kungiyar na Jihar Kano, Dakta Farouk Umar shi ya bayyana wa ‘yan jarida hakan a ranar Lahadin da ta gabata. Ya ce manufar yin hakan shi ne, dattaunawa da ‘yan takarar domin jin abubuwan da za su yi wa jihar idan aka zabe su.

  • Abin Da Muka Tattauna Da Ganduje A Landan — Ja’afar Ja’afar

Ya ce, “A cikin sharuddan da muka ginda ya musa a lokacin da suka samu nasara ban da yin katsalandan a cikin harkokin kudaden kananan hukumomin jihar da muke da su.

“Sannan na biyu, mun bukaci su da su tabbatar da cewa a cikin jami’ansu tun daga kan kwamishinoni da babban sakatarori da shugabannin ma’aikatu kar su kai ‘ya’yansu karatu waje, su tabbatar sun yi karatu a makarantun gwamnati saboda su san matsalolin da suka turnike harkokin iliminmu.

“Haka kuma mun bukaci su tabbatar da cewa babu rikice-rikice a yakin neman zabensu, domin mu samu kamfen mai cike da zaman lafiya da kuma zabe, sannan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar zaman lafiya tare da kin yin amfani da ‘yan daba wajen kamfen dinsu.”

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Bisa zirgin da ake yi kan harkokin siyasar Kano wajen kai hare-hare da abokan hamayya da yin amfani da ‘yan daba, ta sa ita kungiyar ACF rashen jihar ta gindaya wadannan sharudde a tsakanin ‘yan takara, domin samun damar tattaunawa da su wajen samun zaman lafiya da lumana a cikin harkokin siyasar jihar.

Masu ruwa da tsaki a cikin harkokin siyasa su ne suka gana da kungiyar ACF tare da bayyana musu cewa su ja kannuan ‘yan siyasar jihar wajen samun zaman lafiya yayin gudanar da harkokin siyasa a cikin jihar.

Da yake jawabi bayan ganawar sirri da dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Aminu Abdussalam, daya daga cikin shugabannin kungiyar, Farfesa Kamilu Sani Fagge ya bayyana cewa akwai fargaba game da abubuwan da suke faruwa a siyasar Jihar Kano.

Ya ce, “A matsayinmu na dattawa dole mu nuna wa wadannan ‘yan takara abubuwan da muke so da kuma wadanda ba ma so masu kawo tashin hankali da tarwaza zaman lafiya, ba za mu taba hade hannu ba mu bari ana gudanar da gubataccen siyasa a Jihar Kano.”
Fagge ya kara da cewa sun tattauna da ‘yan takarar gwamna domin kokarin samar da zaman lafiya da hanyar dakile rikice-rikice.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Kagara Sandar Girma Ya Gudana

Next Post

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.