• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharuddan Da ACF Ke Son Duk Mai Neman Ya Gaji Ganduje Ya Cika

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Hanya Mafi Sauki Ta Magance Matsalolin Sashin Shari’a – Ganduje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa ta ACF reshen Jihar Kano ta gindaya sharudda ga dukkan ‘yan takarar gwamna da ke jam’iyyu daban-daban wadanda suke son gadar Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a 2023.

Shugaban kungiyar na Jihar Kano, Dakta Farouk Umar shi ya bayyana wa ‘yan jarida hakan a ranar Lahadin da ta gabata. Ya ce manufar yin hakan shi ne, dattaunawa da ‘yan takarar domin jin abubuwan da za su yi wa jihar idan aka zabe su.

  • Abin Da Muka Tattauna Da Ganduje A Landan — Ja’afar Ja’afar

Ya ce, “A cikin sharuddan da muka ginda ya musa a lokacin da suka samu nasara ban da yin katsalandan a cikin harkokin kudaden kananan hukumomin jihar da muke da su.

“Sannan na biyu, mun bukaci su da su tabbatar da cewa a cikin jami’ansu tun daga kan kwamishinoni da babban sakatarori da shugabannin ma’aikatu kar su kai ‘ya’yansu karatu waje, su tabbatar sun yi karatu a makarantun gwamnati saboda su san matsalolin da suka turnike harkokin iliminmu.

“Haka kuma mun bukaci su tabbatar da cewa babu rikice-rikice a yakin neman zabensu, domin mu samu kamfen mai cike da zaman lafiya da kuma zabe, sannan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar zaman lafiya tare da kin yin amfani da ‘yan daba wajen kamfen dinsu.”

Labarai Masu Nasaba

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Bisa zirgin da ake yi kan harkokin siyasar Kano wajen kai hare-hare da abokan hamayya da yin amfani da ‘yan daba, ta sa ita kungiyar ACF rashen jihar ta gindaya wadannan sharudde a tsakanin ‘yan takara, domin samun damar tattaunawa da su wajen samun zaman lafiya da lumana a cikin harkokin siyasar jihar.

Masu ruwa da tsaki a cikin harkokin siyasa su ne suka gana da kungiyar ACF tare da bayyana musu cewa su ja kannuan ‘yan siyasar jihar wajen samun zaman lafiya yayin gudanar da harkokin siyasa a cikin jihar.

Da yake jawabi bayan ganawar sirri da dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Aminu Abdussalam, daya daga cikin shugabannin kungiyar, Farfesa Kamilu Sani Fagge ya bayyana cewa akwai fargaba game da abubuwan da suke faruwa a siyasar Jihar Kano.

Ya ce, “A matsayinmu na dattawa dole mu nuna wa wadannan ‘yan takara abubuwan da muke so da kuma wadanda ba ma so masu kawo tashin hankali da tarwaza zaman lafiya, ba za mu taba hade hannu ba mu bari ana gudanar da gubataccen siyasa a Jihar Kano.”
Fagge ya kara da cewa sun tattauna da ‘yan takarar gwamna domin kokarin samar da zaman lafiya da hanyar dakile rikice-rikice.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Kagara Sandar Girma Ya Gudana

Next Post

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Related

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

5 hours ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

6 hours ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

3 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

3 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

4 weeks ago
Next Post
Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.