• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharuddan Da ACF Ke Son Duk Mai Neman Ya Gaji Ganduje Ya Cika

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
ACF

Kungiyar Dattawan Arewa ta ACF reshen Jihar Kano ta gindaya sharudda ga dukkan ‘yan takarar gwamna da ke jam’iyyu daban-daban wadanda suke son gadar Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a 2023.

Shugaban kungiyar na Jihar Kano, Dakta Farouk Umar shi ya bayyana wa ‘yan jarida hakan a ranar Lahadin da ta gabata. Ya ce manufar yin hakan shi ne, dattaunawa da ‘yan takarar domin jin abubuwan da za su yi wa jihar idan aka zabe su.

  • Abin Da Muka Tattauna Da Ganduje A Landan — Ja’afar Ja’afar

Ya ce, “A cikin sharuddan da muka ginda ya musa a lokacin da suka samu nasara ban da yin katsalandan a cikin harkokin kudaden kananan hukumomin jihar da muke da su.

“Sannan na biyu, mun bukaci su da su tabbatar da cewa a cikin jami’ansu tun daga kan kwamishinoni da babban sakatarori da shugabannin ma’aikatu kar su kai ‘ya’yansu karatu waje, su tabbatar sun yi karatu a makarantun gwamnati saboda su san matsalolin da suka turnike harkokin iliminmu.

“Haka kuma mun bukaci su tabbatar da cewa babu rikice-rikice a yakin neman zabensu, domin mu samu kamfen mai cike da zaman lafiya da kuma zabe, sannan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar zaman lafiya tare da kin yin amfani da ‘yan daba wajen kamfen dinsu.”

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Bisa zirgin da ake yi kan harkokin siyasar Kano wajen kai hare-hare da abokan hamayya da yin amfani da ‘yan daba, ta sa ita kungiyar ACF rashen jihar ta gindaya wadannan sharudde a tsakanin ‘yan takara, domin samun damar tattaunawa da su wajen samun zaman lafiya da lumana a cikin harkokin siyasar jihar.

Masu ruwa da tsaki a cikin harkokin siyasa su ne suka gana da kungiyar ACF tare da bayyana musu cewa su ja kannuan ‘yan siyasar jihar wajen samun zaman lafiya yayin gudanar da harkokin siyasa a cikin jihar.

Da yake jawabi bayan ganawar sirri da dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Aminu Abdussalam, daya daga cikin shugabannin kungiyar, Farfesa Kamilu Sani Fagge ya bayyana cewa akwai fargaba game da abubuwan da suke faruwa a siyasar Jihar Kano.

Ya ce, “A matsayinmu na dattawa dole mu nuna wa wadannan ‘yan takara abubuwan da muke so da kuma wadanda ba ma so masu kawo tashin hankali da tarwaza zaman lafiya, ba za mu taba hade hannu ba mu bari ana gudanar da gubataccen siyasa a Jihar Kano.”
Fagge ya kara da cewa sun tattauna da ‘yan takarar gwamna domin kokarin samar da zaman lafiya da hanyar dakile rikice-rikice.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

LABARAI MASU NASABA

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.