• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharuddan Da ACF Ke Son Duk Mai Neman Ya Gaji Ganduje Ya Cika

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Hanya Mafi Sauki Ta Magance Matsalolin Sashin Shari’a – Ganduje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa ta ACF reshen Jihar Kano ta gindaya sharudda ga dukkan ‘yan takarar gwamna da ke jam’iyyu daban-daban wadanda suke son gadar Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a 2023.

Shugaban kungiyar na Jihar Kano, Dakta Farouk Umar shi ya bayyana wa ‘yan jarida hakan a ranar Lahadin da ta gabata. Ya ce manufar yin hakan shi ne, dattaunawa da ‘yan takarar domin jin abubuwan da za su yi wa jihar idan aka zabe su.

  • Abin Da Muka Tattauna Da Ganduje A Landan — Ja’afar Ja’afar

Ya ce, “A cikin sharuddan da muka ginda ya musa a lokacin da suka samu nasara ban da yin katsalandan a cikin harkokin kudaden kananan hukumomin jihar da muke da su.

“Sannan na biyu, mun bukaci su da su tabbatar da cewa a cikin jami’ansu tun daga kan kwamishinoni da babban sakatarori da shugabannin ma’aikatu kar su kai ‘ya’yansu karatu waje, su tabbatar sun yi karatu a makarantun gwamnati saboda su san matsalolin da suka turnike harkokin iliminmu.

“Haka kuma mun bukaci su tabbatar da cewa babu rikice-rikice a yakin neman zabensu, domin mu samu kamfen mai cike da zaman lafiya da kuma zabe, sannan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar zaman lafiya tare da kin yin amfani da ‘yan daba wajen kamfen dinsu.”

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Bisa zirgin da ake yi kan harkokin siyasar Kano wajen kai hare-hare da abokan hamayya da yin amfani da ‘yan daba, ta sa ita kungiyar ACF rashen jihar ta gindaya wadannan sharudde a tsakanin ‘yan takara, domin samun damar tattaunawa da su wajen samun zaman lafiya da lumana a cikin harkokin siyasar jihar.

Masu ruwa da tsaki a cikin harkokin siyasa su ne suka gana da kungiyar ACF tare da bayyana musu cewa su ja kannuan ‘yan siyasar jihar wajen samun zaman lafiya yayin gudanar da harkokin siyasa a cikin jihar.

Da yake jawabi bayan ganawar sirri da dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Aminu Abdussalam, daya daga cikin shugabannin kungiyar, Farfesa Kamilu Sani Fagge ya bayyana cewa akwai fargaba game da abubuwan da suke faruwa a siyasar Jihar Kano.

Ya ce, “A matsayinmu na dattawa dole mu nuna wa wadannan ‘yan takara abubuwan da muke so da kuma wadanda ba ma so masu kawo tashin hankali da tarwaza zaman lafiya, ba za mu taba hade hannu ba mu bari ana gudanar da gubataccen siyasa a Jihar Kano.”
Fagge ya kara da cewa sun tattauna da ‘yan takarar gwamna domin kokarin samar da zaman lafiya da hanyar dakile rikice-rikice.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Kagara Sandar Girma Ya Gudana

Next Post

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

19 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
ACF
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.