Da safiyar yau Alhamis 25 ga wata, mukaddashiyar shugaban kasar Venezuela, Delcy Rodríguez, ta yi jawabi ga kasa kai-tsaye ta gidan talabijin na kasar, inda ta yi bayani kan yanayin barnar girgizar kasar da ta abku tare da yin kiran hadin kan kasa domin tunkarar wannan ibtila’i daga indallahi.
A cikin jawabin nata, ta bayyana godiya ga gwamnatin Sin bisa aniyarta ta bayar da taimako ga Venezuela.
Da misalin karfe 6:00 na yammacin jiya 24 ga watan nan, Venezuela ta fuskanci girgizar kasa guda biyu bi-da-bi, da suka kai karfin maki 7 ko fiye da haka. A cewar sabuwar sanarwar da mahukunta daga Venezuelar suka fitar a yau 25 ga wata, wannan girgizar kasa ta yi sanadin mutuwar mutane akalla 164, tare da jikkata sama da 900. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














