A wani taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar a yau 25 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar kasuwancin kasar Sin, He Yadong, ya ce bisa yarjejeniyar fahimtar juna da aka cimma a tattaunawar tattalin arziki da kasuwanci tsakanin Sin da Amurka, bangarorin biyu sun amince da kafa majalisar kasuwanci, inda za a tattauna batutuwan hadin gwiwa, ciki har da rage haraji bisa daidaito a karkashin majalisar.
Haka kuma, He Yadong ya ce sabbin matakan da gwamnatin Amurka ta dauka na kara wasu kamfanonin Sin a cikin jerin sunayen abin da ta kira “kamfanonin masu nasaba da sojin Sin” na haifar da babbar illa ga hakkoki da kuma muradun kamfanonin Sin, don haka Sin ta dauki matakan mayar da martani.
Ma’aikatar kasuwancin Sin ta fitar da sanarwa a ranar 22 ga watan Yuni, inda ta kara wasu kamfanoni 10 na Amurka cikin jerin wadanda aka sanya wa takunkumin fitar da kayayyaki bisa doka. A ranar da aka yi hakan kuma, ma’aikatar kudi ta Sin ta fitar da sanarwa cewa, bisa doka, ba za a sayi kayayyakin da kamfanoni 46 na Amurka ke samarwa ba, a cikin tsarin sayayyar kayayyakin gwamnati.
Wadannan kamfanonin na Amurka da abin ya shafa duk suna da alaka da harkokin soja. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














