Shugabar kasar Namibia, Netumbo Nandi-Ndaitwah, ta halarci wani biki a ranar Laraba a birnin Ondangwa da ke arewacin kasar, domin murnar daga darajar cibiyar kirkire-kirkire da al’adu ta Ondangwa, da kuma sabon dakin baje kolin kimiyya da aka gina ta cibiyar.
Nandi-Ndaitwah ta bayyana a wajen taron cewa, “Dangantaka tsakanin Namibia da kasar Sin ta ginu ce bisa mutunta juna, da muradu na bai-daya, da kuma jajircewarsu iri daya wajen samun ci gaba.”
Cibiyar Rossing Foundation da kamfanin Rossing Uranium Limited, wanda kamfanin sarrafa nukiliya na kasar Sin (CNNC) ke da kaso mafi rinjaye na mallakarsa ne suka yi hadin gwiwa wajen gina cibiyar ta kirkire-kirkire da al’adu ta Ondangwa, domin daga dajarar wuraren ba da ilimi da na ayyukan ci gaba na al’ummar yankin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














