Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kamata ya yi a gaggauta bude mashigin Hormuz, ta yadda jiragen ruwa za su koma zirga-zirga ba tare da wani kai’di ba, don tabbatar da daidaiton ayyukan masana’antu da tsarin hada-hadar samar da hajoji.
Wang Yi, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya yi kiran ne a jiya Laraba yayin tattaunawa ta wayar tarho da mataimakin firaministan kasar Pakistan, kana ministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishaq Dar.
Wang ya godewa bangaren Pakistan, bisa gaggauta sanar da Sin sabon matakin tattaunawa da aka shiga tsakanin Iran da Amurka. Ya ce an shiga sabon babin cimma zaman lafiya, duk da cewa tafiya ce mai nisa, wadda ka iya zama mai sarkakiya kuma mai wahala.
Amma duk da haka, har kullum Sin za ta ci gaba da goyon bayan Pakistan, da sauran kasashe abokan tafiya wajen ci gaba da taka rawar gani, da zama cikin shirin wanzar da tuntubar juna ta kut da kut, da aiwatar da tsare-tsare tare da Pakistan.
Ministan harkokin wajen kasar ta Sin, ya kara da cewa bai dace yankin Gabas ta Tsakiya, ciki har da yankin Gulf, ya ci gaba da kasancewa fage na gasar nuna karfin tuwo, ko zama fage na aiwatar da siyasar shiyya ba, kuma kamata ya yi kasashen yankin su rungumi manufofi na cin gashin kai da rike makomarsu a hannuwansu. (Saminu Alhassan)














