Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da kafa wani Kwamitin Musamman Kan Miyagun Ƙwayoyi da Safararsu Ba Bisa Ka’ida Ba, a wani mataki na ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da laifukan da ke da alaƙa da su a jihar.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Alhamis.
Sanarwar ta bayyana cewa an naɗa Muhuyi Magaji Rimin gado a matsayin shugaban wannan sabon kwamitin na musamman.Muhuyi shi ne tsohon Shugaban Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafen Al’umma da Yaki Da Cin Hanci, kuma ana kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin fitattun masu yaƙi da cin hanci da rashawa a jihar.
Gwamnatin jihar ta bayyana cewa an kafa kwamitin ne domin samar da haɗin gwiwa tsakanin hukumomi daban-daban wajen Tarwatsa hanyoyin safarar miyagun ƙwayoyi da cibiyoyin masu fataucinsu; Hanzarta gurfanar da masu laifi a gaban kotu; Rage yawan masu amfani da miyagun ƙwayoyi ta hanyar wayar da kai da ilimantar da al’umma.
Matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Kano na magance matsalar shaye-shaye, musamman a tsakanin matasa, da kuma rage tasirin laifukan da ke da alaƙa da miyagun ƙwayoyi a cikin al’umma.













