Ƙungiyar Dandalin Hadin Kai da ci gaban Kansiloli ta Kasa ‘National Progressives Councillors’ Forum (NPCF)’, mai wakiltar kansilolin jam’iyyar APC sama da 10,000 a faɗin ƙasar nan, ta buƙaci Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya sa a dakatar da abin da ta kira bincike da zarge-zargen siyasa da ake yi wa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar.
Ƙungiyar ta bayyana cewa zargin da ke alaƙanta Sanata Yari da kama ɗanyen zinari na kimanin naira biliyan 4.4 a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano ba shi da tushe, tana mai cewa sunayen waɗanda ake zargi da lamarin da EFCC ta bayyana ba su haɗa da sunansa ba. Haka kuma, ta musanta zargin cewa Sanatan na tallafa wa zanga-zangar adawa da gwamnati ko wata jam’iyyar adawa.
NPCF ta yabawa irin ayyukan ci gaba da Sanata Yari ya aiwatar lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara da kuma gudunmawar da yake bayarwa a matsayin Sanata mai wakiltar Zamfara ta Yamma.
Ƙungiyar ta kuma zargi wasu ’yan siyasa da amfani da tasirinsu wajen matsa wa Sanata Yari lamba saboda dalilan siyasa, tana mai cewa hakan na iya shafar haɗin kai da zaman lafiyar jam’iyyar APC.
A ƙarshe, ƙungiyar ta tabbatar da goyon bayanta ga gwamnatin Shugaba Tinubu, amma ta yi gargaɗin cewa idan ba a dakatar da abin da ta kira yaƙin ɓata suna da zarge-zargen marasa tushe kan Sanata Yari ba, za ta sake nazarin irin goyon bayan da take bai wa jam’iyyar APC.














