• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shinge 4 Da Sabon Gwamnan Zamfara Ya Tsallake Kafin Ya Doke Matawalle

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Shinge 4 Da Sabon Gwamnan Zamfara Ya Tsallake Kafin Ya Doke Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata 21 ga watan Maris 2023 ne al’ummar Nijeriya suka tashi da labarin wata girgiza fagen siyasar kasar nan, inda aka sanar da cewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP Dakta Dauda Lawal Dare, ya lashe zaben da aka yi na gwamna a ranar 18 ga watan Maris 2023 a Jihar Zamfara, inda ya yi waje rod da gwamna mai ci na jam’iyyar APC, Daklta Bello Matawalle.

Jami’in kula da zaben da aka yi, Farfesa Kasimu Shehu, ya sanar da cewa, sakamakon zaben da aka yi ya nuna cewa, Dauda Dare ya samu kuri’a 377,726 inda ya kayar da Matawalle wanda ya tashi da kuri’a 311,976.

  • Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana
  • Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Tuni aka barke da murnar wannan nasarar da Lawal na PDP ya samu a sassan jihar Zamfara dama Nijeriya baki daya, nasarar da ake gani lallai ta samu ne ta hanyar jajircewa da aiki tukuru daga Dan takarar Dakta Lawal da bangaren jam’iyyar PDP gaba daya.

Tabbas wannan nasarar ta Dauda Lawal bata zo da sauki ba, ya ci karo da shingaye da dama. Dauda wanda tsohon ma’aikacin Banki ne ya fuskanci shari’u da dama har zuwa makonni kadan kafin a fuskanci zaben, shari’un neman tabbatar da shi a matsayin dan takarar gwamnan Zamfara, amma cikin ikon Allah ya samu nasara a dukkan shari’un da ya fuskanta.

Tun farko a watan Satumba na shekarar 20022, wata kotun tarayya da ke Gusau ta soke takararsa kan cewa, taron da aka yi inda aka zabe shi a mastayin dan takarar ba halastacciya ba ne, wani tsohon dan majalisar tarayya ne mai suna Alhaji Ibrahim Shehu Gusau, ya nemi kotu ta soke zaben, a cewarsa an tafka magudi a zabukkan da aka yi. Maishari’a Aminu Bappa ya soke zaben a ranar 25 ga wata Mayu 2022 inda ya nemi a sake gudanar da wani zaben fidda gwani.

Labarai Masu Nasaba

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

Duk da cewa, Lawal ya sake lashe zaben fidda gwani da aka yi amma kotun ta kuma dakatar da aiwatar da zaben sa da aka yi.

Haka kuma Maishari’a Bappa ya sake soke zaben ya kuma zartar da cewa, jam’iyyar PDP ba za ta iya gabatar da dan takarar a jihar Zamfara a zaben 2023 gaba daya ba.

Amma Lawal bai sadakar ba, inda shi da Adamu Maina-Waziri, shugaban kwamitin da ya gudanar da zaben fidda gwamni Kanal Bala Mande (mai Ritaya) suka daukaka kara a babban kotun daukaka kara na Sakwatto inda suka nemi kotu da soke umarnin.

A watan Janairu na 2023 babbar kotun a karkashin Maishari’a Abubakar Talba, ta yi watsi da hukunci inda ta sake amincewa da Dakta Lawal a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP a zaben da za a yi.

Karin shinge

Duk da wadannan nasarorin da Lawal ya samu, sai gashi an daukaka karar zuwa kotun koli. Inda a ranar 6 ga watan Maris 2023, ya sake samun nasarar a kotun koli inda ta zartar da cewa, Lawal ne halastaccen dan takarar jam’iyyar PDP kuma shi ne zai tsaya mata takara a zaben 2023.

Haka kuma Lawal ya fuskanci shari’a daga hukumar EFCC, inda shari’ar ta kai ga kotun koli amma cikin ikon Allah Lawal ya samu cikakken nasara inda kotun ta wanke shi daga dukkan zarge-zarge.

Daga ranar 29 ga watan Mayu na shekarar 2023 Dakta Lawal Dare zai karbi ragamar mulki Jihar Zamfara daga hannun Bello Matawale inda zai cigaba da aiwatar da alkawuran da ya yi wa la’umma, muna fatan al’umma za su bashi dukkan goyon bayan da yake bukata don kai Jihar Zamfa tudun-mun-tsira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DareMatawalleZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Darussan Da ‘Yan Siyasa Za Su Koya A Zaben 2023

Next Post

Tarihin Mamayar Tattar 4

Related

'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

1 week ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

1 week ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

1 week ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

2 weeks ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 weeks ago
Next Post
Tarihin Mamayar Tattar 4

Tarihin Mamayar Tattar 4

LABARAI MASU NASABA

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.