ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shinge 4 Da Sabon Gwamnan Zamfara Ya Tsallake Kafin Ya Doke Matawalle

by Bello Hamza
3 years ago
Zamfara

A ranar Talata 21 ga watan Maris 2023 ne al’ummar Nijeriya suka tashi da labarin wata girgiza fagen siyasar kasar nan, inda aka sanar da cewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP Dakta Dauda Lawal Dare, ya lashe zaben da aka yi na gwamna a ranar 18 ga watan Maris 2023 a Jihar Zamfara, inda ya yi waje rod da gwamna mai ci na jam’iyyar APC, Daklta Bello Matawalle.

Jami’in kula da zaben da aka yi, Farfesa Kasimu Shehu, ya sanar da cewa, sakamakon zaben da aka yi ya nuna cewa, Dauda Dare ya samu kuri’a 377,726 inda ya kayar da Matawalle wanda ya tashi da kuri’a 311,976.

  • Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana
  • Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Tuni aka barke da murnar wannan nasarar da Lawal na PDP ya samu a sassan jihar Zamfara dama Nijeriya baki daya, nasarar da ake gani lallai ta samu ne ta hanyar jajircewa da aiki tukuru daga Dan takarar Dakta Lawal da bangaren jam’iyyar PDP gaba daya.

ADVERTISEMENT

Tabbas wannan nasarar ta Dauda Lawal bata zo da sauki ba, ya ci karo da shingaye da dama. Dauda wanda tsohon ma’aikacin Banki ne ya fuskanci shari’u da dama har zuwa makonni kadan kafin a fuskanci zaben, shari’un neman tabbatar da shi a matsayin dan takarar gwamnan Zamfara, amma cikin ikon Allah ya samu nasara a dukkan shari’un da ya fuskanta.

Tun farko a watan Satumba na shekarar 20022, wata kotun tarayya da ke Gusau ta soke takararsa kan cewa, taron da aka yi inda aka zabe shi a mastayin dan takarar ba halastacciya ba ne, wani tsohon dan majalisar tarayya ne mai suna Alhaji Ibrahim Shehu Gusau, ya nemi kotu ta soke zaben, a cewarsa an tafka magudi a zabukkan da aka yi. Maishari’a Aminu Bappa ya soke zaben a ranar 25 ga wata Mayu 2022 inda ya nemi a sake gudanar da wani zaben fidda gwani.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Duk da cewa, Lawal ya sake lashe zaben fidda gwani da aka yi amma kotun ta kuma dakatar da aiwatar da zaben sa da aka yi.

Haka kuma Maishari’a Bappa ya sake soke zaben ya kuma zartar da cewa, jam’iyyar PDP ba za ta iya gabatar da dan takarar a jihar Zamfara a zaben 2023 gaba daya ba.

Amma Lawal bai sadakar ba, inda shi da Adamu Maina-Waziri, shugaban kwamitin da ya gudanar da zaben fidda gwamni Kanal Bala Mande (mai Ritaya) suka daukaka kara a babban kotun daukaka kara na Sakwatto inda suka nemi kotu da soke umarnin.

A watan Janairu na 2023 babbar kotun a karkashin Maishari’a Abubakar Talba, ta yi watsi da hukunci inda ta sake amincewa da Dakta Lawal a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP a zaben da za a yi.

Karin shinge

Duk da wadannan nasarorin da Lawal ya samu, sai gashi an daukaka karar zuwa kotun koli. Inda a ranar 6 ga watan Maris 2023, ya sake samun nasarar a kotun koli inda ta zartar da cewa, Lawal ne halastaccen dan takarar jam’iyyar PDP kuma shi ne zai tsaya mata takara a zaben 2023.

Haka kuma Lawal ya fuskanci shari’a daga hukumar EFCC, inda shari’ar ta kai ga kotun koli amma cikin ikon Allah Lawal ya samu cikakken nasara inda kotun ta wanke shi daga dukkan zarge-zarge.

Daga ranar 29 ga watan Mayu na shekarar 2023 Dakta Lawal Dare zai karbi ragamar mulki Jihar Zamfara daga hannun Bello Matawale inda zai cigaba da aiwatar da alkawuran da ya yi wa la’umma, muna fatan al’umma za su bashi dukkan goyon bayan da yake bukata don kai Jihar Zamfa tudun-mun-tsira.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Next Post
Tarihin Mamayar Tattar 4

Tarihin Mamayar Tattar 4

LABARAI MASU NASABA

Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.