ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Sin Da Rasha Sun Yi Taron Manema Labarai Na Hadin Gwiwa

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A yau Alhamis shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin sun gudanar da taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Beijing.

A yayin taron, shugaba Xi ya jaddada cewa, a bana ake cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Rasha. Kuma dangantakar sassan biyu ta zamo muhimmin misali na sabon salon alakar kasa da kasa, da kuma kyakkyawan kawancen manyan kasashe biyu dake makwaftaka da juna. Ya ce, ci gaban bunkasar alakar sassan biyu, na da nasaba da yadda suke dora muhimmanci ga ka’idoji 5.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara
  • Amurka Za Ta Lashe Amanta Game Da Karin Harajin Rashin Adalci Da Ta Bugawa Kasar Sin

Na farko, shugaba Xi ya ce, Sin da Rasha, na dora muhimmanci ga martaba juna a matsayin jigon alakarsu, kuma har kullum suna goyon bayan juna wajen kare manyan muradunsu. Na biyu kuma, sassan biyu suna rungumar hadin gwiwar cimma moriyar juna, a matsayin karfin dake ingiza kawancensu, da aiki wajen yaukaka sabon salon cimma moriya tare. Na uku kuma, Sin da Rasha na kara azamar wanzar da abota a matsayin tushen dangantakarsu, da ingiza kawancensu zuwa mataki na gaba. Na hudu kuma, kasashen biyu na rungume da manufar kyautata tsare-tsare bisa matsayin koli, a matsayin hanyar tabbatar da kawance, da karkata akalar jagorancin duniya zuwa turba ta gari. Na biyar kuma, Sin da Rasha sun himmantu wajen tabbatar da daidaito, da adalci, a matsayin dalilin bunkasa alakokinsu, da mayar da hankali ga warware batutuwa masu jan hankali ta hanyar siyasa.

ADVERTISEMENT

Sannan a yau shugaban kasar Sin Xi Jinping, da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin sun halarci bikin kaddamar da shekarar al’adun Sin da Rasha, da bikin kide-kide da raye-raye na musamman, wanda aka shirya a birnin Beijing, domin murna cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Rasha.

A bana, sassan biyu na Sin da Rasha za su gudanar da ayyukan musayar al’adu masu kayatarwa, don zurfafa hadin gwiwar musayar al’adunsu, da aiki tare, wajen bude sabon babin ingiza musayar al’adu tsakanin Sin da Rasha.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Bugu da kari, a yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Rasha Vladimir Putin sun sa hannu, da kuma gabatar da wata hadaddiyar sanarwa, game da karfafa dangantakar abokantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a sabon zamani tsakanin jamhuriyar jama’ar kasar Sin da tarayyar Rasha, yayin da ake cika shekaru 75 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasahsen biyu. (Saminu Alhassan, Safiyah Ma)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi

Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.