Wata sanarwar hadin gwiwa da aka fitar a Talatar nan ta ce kasar Sin da kungiyar tarayyar Turai ta EU, sun kaddamar da tsarin tuntuba dangane da harkokin cinikayya da zuba jari a hukumance, har ma sassan biyu sun gudanar da taron farko karkashin tsarin.
Sanarwar ta ce sassan biyu sun fayyace bangarorin aiki hudu karkashin tsarin, wadanda suka hada da daidaita fannonin cinikayya da zuba jari, da rike ragamar fitar da hajoji, da batun ikon mallakar fasaha, da aiwatar da sauye-sauye a kungiyar cinikayya ta duniya ko WTO.
Ministan ma’aikatar cinikayya ta Sin Wang Wentao, da kwamishinan EU mai lura da hada-hadar cinikayya, da kare tattalin arziki, da alakar hukumomi, da tabbatar da gudanar da komai a bude Maros Šefčovič ne suka jagoranci taron na farko, wanda ya gudana jiya Litinin a birni Brussels.Sassan biyu sun gudanar da cikakkiyar tattaunawa mai zurfi da ma’ana dangane da muhimman batutuwan tattalin arziki da cinikayya. Kana sun amince da kafa tsarin sanya ido na hadin gwiwa tsakaninsu. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)














