• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Tsohon Shugaban Kasar Sudan Omar el-Bashir

byRabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Omar el-Bashir

An haifi shugaban kasar ta Sudan Omar al-Hassan Ahmad Bashir a shekara ta 1945 a garin Hoshe Bannaga mai tazarar kilomita 100 daga yankin Arewa maso Gabashin birnin Khartoum.

Ya kuma fara karatunsa na babar makarantar Middile ta Ahlia dake garin Shendi, daga nan ne kuma mahaifansa suka yi kaura zuwa birnin Khartoum a can din kuma ya kammala iliminsa na sakandre.

  • Mun Dauki Matakan Fito-na-fito Da Masu Kawo Gurbataccen Taki A Kasuwarmu – Masu Sayar Da Taki

Shugaban kasar dai ta Sudan ya ci gaba da daukar nauyin karatunsa ne da irin taimakon da yake samu na kudade daga mahaifansa da kuma dan abin da yake samu a lokacin da ya yi aiki a wani garejin gayaran motoci a birnin na Khartoum.

Bayan da shugaban kasar ta Sudan Omar al-Bashir ya kammala iliminsa na sakandre, ya shiga makarantar horar da sojin sama ta kasar Sudan, inda har ya sami horo na tuka jirgin sama.

A nan din ne kuma sami baban mukami a tskanin dakarun saman kasar Sudan, kafin kuma daga bisani ya zama shugaban Brigade din sojojin kasa na kasar Sudan.
Tsohon shugaban Kasar Sudan Omar Hassan Ahmad al-Bashir, ya sami manyan degrori biyu na Masters a fanin kimiyyar ayyukan soji, a kwalegen horars da kwamandojin soji ta Sudan da kuma kasar Malaysiya.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Haka zalika al-Bashir ya halarci kwalejin horas da soji ta birnin Cairo,inda har ya shiga cikin sojin kasar Masar, a lokacin da masar din ta yi yaki da Isra’ila a shekara ta 1973.
A shekara ta 1988, an nada Omar al-Bashir kan mukamin kwamandan Birgde ta 8 ta sojin Sudan a yankin Kudancin Sudan, inda aka dora masa alhakin yaki da yan tawayen Kudancin Sudan.

A watan Yuni na 1988 shida wasu manyan hafsoshin soji, sun hambarar da zababbiyar gwamnatin hadin kan kasa, karkashin shugabancin Sadik Al-Mahdi.

Manufofin gwamnatin Al-Bashir game da dabaka tsarin shariar musulunci a Sudan, ta haifar masa da rashin fahimtar juna tsakaninsa da alumomin Kudancin Sudan da mafi yawansu suka kasance Kiristoci, wanan dalili ne ma ya kara rura wutar fadan yan tawayen Kudancin Sudan.

A lokacin da Janar al-Bashir ya karbi ragamar mulkin Sudan ta hanyar juyin mulki irin na soji a ranar 30 ga watan Yunin 1989, an rika tabbatar da cewa anya al-Bashir zai iya rike ragamar mulkin kasar ta Sudan da yakin basasa ya daidaita.

A lokacin da al-Bashir ya karbi ragamar mulkin Sudan yana da shekaru 42 a duniya, kuma shi ne din ke zaman jami’in soji na farko da suka taka muhimiyar rawa wajen kai farmaki kan alumomin Kudancin Sudan.
Kasar dai ta Sudan an kasa ta kashi biyu, tsakanin Larabawa Musulmi na Arewaci da kuma kiristoci dake zaune a Kudancin na Sudan.

Kungiyar ‘yan tawayen Sudan ta SPLA ta fara yakin neman ‘yanci ne a shekara ta 1983, kuma tun daga wanan lokacin ne, kafin ma mulkin al-Bashir gwamnatocin da suka gabata, sun yi yaki da ‘yan tawayen Kudancin Sudan.

Kungiyar Afuwa ta Duniya ta kiyasta cewa, kimanin al’ummar kasar ta Sudan miliyan daya suka rasa rayukan su, sakamakon yakin basasar da ya barke a kasar, yayin kuma al’ummar ta Sudan miliyan 4.5 suka yi gudun hijira, zuwa wasu kasahe na ketare don tsira da rayukansu.

A lokacin da al-Bashir ya karbi ragamar mulki daga Sadek al-Mahdi a shekara ta 1989, da sunan ceto kasar Sudan daga hali na kaka na ka yi da ta sami kanta a ciki, ya sami goyon bayan Hassan al-Turabi shugaban jama’iyar National Islamic Front, kafin kuma daga karshe suka raba gari da juna, a lokacin da al-bashir ya rushe majalisar dokokin Sudan, ya kuma dauki matakai na soke dukanin jama’iyun siyasa dama kafofin yada labarun Sudan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Matawalle Ya Gwangwaje Jama’ar Zamfara Da Rabon Shanu Da Ragunan Layya

Matawalle Ya Gwangwaje Jama'ar Zamfara Da Rabon Shanu Da Ragunan Layya

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version