• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Tsohon Shugaban Kasar Sudan Omar el-Bashir

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Omar el-Bashir

An haifi shugaban kasar ta Sudan Omar al-Hassan Ahmad Bashir a shekara ta 1945 a garin Hoshe Bannaga mai tazarar kilomita 100 daga yankin Arewa maso Gabashin birnin Khartoum.

Ya kuma fara karatunsa na babar makarantar Middile ta Ahlia dake garin Shendi, daga nan ne kuma mahaifansa suka yi kaura zuwa birnin Khartoum a can din kuma ya kammala iliminsa na sakandre.

  • Mun Dauki Matakan Fito-na-fito Da Masu Kawo Gurbataccen Taki A Kasuwarmu – Masu Sayar Da Taki

Shugaban kasar dai ta Sudan ya ci gaba da daukar nauyin karatunsa ne da irin taimakon da yake samu na kudade daga mahaifansa da kuma dan abin da yake samu a lokacin da ya yi aiki a wani garejin gayaran motoci a birnin na Khartoum.

Bayan da shugaban kasar ta Sudan Omar al-Bashir ya kammala iliminsa na sakandre, ya shiga makarantar horar da sojin sama ta kasar Sudan, inda har ya sami horo na tuka jirgin sama.

A nan din ne kuma sami baban mukami a tskanin dakarun saman kasar Sudan, kafin kuma daga bisani ya zama shugaban Brigade din sojojin kasa na kasar Sudan.
Tsohon shugaban Kasar Sudan Omar Hassan Ahmad al-Bashir, ya sami manyan degrori biyu na Masters a fanin kimiyyar ayyukan soji, a kwalegen horars da kwamandojin soji ta Sudan da kuma kasar Malaysiya.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Haka zalika al-Bashir ya halarci kwalejin horas da soji ta birnin Cairo,inda har ya shiga cikin sojin kasar Masar, a lokacin da masar din ta yi yaki da Isra’ila a shekara ta 1973.
A shekara ta 1988, an nada Omar al-Bashir kan mukamin kwamandan Birgde ta 8 ta sojin Sudan a yankin Kudancin Sudan, inda aka dora masa alhakin yaki da yan tawayen Kudancin Sudan.

A watan Yuni na 1988 shida wasu manyan hafsoshin soji, sun hambarar da zababbiyar gwamnatin hadin kan kasa, karkashin shugabancin Sadik Al-Mahdi.

Manufofin gwamnatin Al-Bashir game da dabaka tsarin shariar musulunci a Sudan, ta haifar masa da rashin fahimtar juna tsakaninsa da alumomin Kudancin Sudan da mafi yawansu suka kasance Kiristoci, wanan dalili ne ma ya kara rura wutar fadan yan tawayen Kudancin Sudan.

A lokacin da Janar al-Bashir ya karbi ragamar mulkin Sudan ta hanyar juyin mulki irin na soji a ranar 30 ga watan Yunin 1989, an rika tabbatar da cewa anya al-Bashir zai iya rike ragamar mulkin kasar ta Sudan da yakin basasa ya daidaita.

A lokacin da al-Bashir ya karbi ragamar mulkin Sudan yana da shekaru 42 a duniya, kuma shi ne din ke zaman jami’in soji na farko da suka taka muhimiyar rawa wajen kai farmaki kan alumomin Kudancin Sudan.
Kasar dai ta Sudan an kasa ta kashi biyu, tsakanin Larabawa Musulmi na Arewaci da kuma kiristoci dake zaune a Kudancin na Sudan.

Kungiyar ‘yan tawayen Sudan ta SPLA ta fara yakin neman ‘yanci ne a shekara ta 1983, kuma tun daga wanan lokacin ne, kafin ma mulkin al-Bashir gwamnatocin da suka gabata, sun yi yaki da ‘yan tawayen Kudancin Sudan.

Kungiyar Afuwa ta Duniya ta kiyasta cewa, kimanin al’ummar kasar ta Sudan miliyan daya suka rasa rayukan su, sakamakon yakin basasar da ya barke a kasar, yayin kuma al’ummar ta Sudan miliyan 4.5 suka yi gudun hijira, zuwa wasu kasahe na ketare don tsira da rayukansu.

A lokacin da al-Bashir ya karbi ragamar mulki daga Sadek al-Mahdi a shekara ta 1989, da sunan ceto kasar Sudan daga hali na kaka na ka yi da ta sami kanta a ciki, ya sami goyon bayan Hassan al-Turabi shugaban jama’iyar National Islamic Front, kafin kuma daga karshe suka raba gari da juna, a lokacin da al-bashir ya rushe majalisar dokokin Sudan, ya kuma dauki matakai na soke dukanin jama’iyun siyasa dama kafofin yada labarun Sudan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Next Post
Matawalle Ya Gwangwaje Jama’ar Zamfara Da Rabon Shanu Da Ragunan Layya

Matawalle Ya Gwangwaje Jama'ar Zamfara Da Rabon Shanu Da Ragunan Layya

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.