ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagogin Sin Da Amurka Sun Zurfafa Tattaunawa Game Da Batutuwan Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Amurka

Tawagogin kasar Sin da na Amurka sun gudanar da tattaunawa mai zurfi da ma’ana, sun kuma yi musayar ra’ayoyi da shawarwari dangane da batutuwan tattalin arziki da cinikayya da kasashen biyu suke mayar da hankali a kansu, ciki har da tsare-tsaren harajin fito, da ingiza dangantakar cinikayya da zuba jari, tare da wanzar da sakamako na matakai da suka amincewa bayan tattaunawa.

Jagororin tattaunawar ta wannan karo da ta gudana a ranakun Lahadi da jiya Litinin, sun hada da jagoran tawagar Sin, kuma mataimakin firaministan kasar He Lifeng. Sai kuma bangaren Amurka da ya hada da sakataren baitul-malin kasar Scott Bessent, da wakilin cinikayyar Amurka Jamieson Greer.

Da yake tsokaci yayin sabon zagayen tattaunawar, He Lifeng ya ce, karkashin kyakkyawan tsari na muhimmiyar fahimtar juna tsakanin shugabannin kasashen biyu, da sakamakon zagaye biyar na tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da suka gudanar cikin shekarar da ta gabata, Sin da Amurka sun cimma jerin nasarori a fannonin raya tattalin arziki da na cinikayya.

ADVERTISEMENT

He ya ce, wadannan sakamako sun ingiza babban yanayi na tabbas, da daidaito cikin dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin sassan biyu, da ma tattalin arzikin duniya baki daya. Mataimakin firaministan na Sin ya kara da cewa, har kullum kasar Sin na adawa da matakin kakaba haraji daga bangare guda da Amurka ke aiwatarwa. Yana mai kira gare ta da ta kawar da dukkanin irin wadannan haraji, da ma sauran matakai masu haifar da tarnaki. A cewarsa, Sin za ta aiwatar da matakai na wajibi domin kare halastattun hakkoki da moriyarta.

Kazalika, Sin na fatan Amurka za ta rungumi tafarki na bai daya tare da Sin, ta kuma yi biyayya ga kudurorin musamman da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare da fadada fannonin hadin gwiwa, da takaita matsalolin da suke fuskanta, ta yadda hakan zai ingiza bunkasar alakar tattalin arziki, da cinikayya mai inganci da daidaito tsakanin kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Wakilai daga bangaren Amurka kuwa, sun ce daidaito a yanayin alakar tattalin arziki, da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, na da matukar muhimmanci ga kasashen biyu da ma duniya baki daya, zai kuma tallafa matuka wajen bunkasa tattalin arzikin duniya, da samar da kariya ga tsarin rarraba hajoji zuwa sassan kasa da kasa, da daidaito ga hada-hadar kudade. Bangaren na Amurka, ya kuma bayyana bukatar magance takun-saka, da dakile kara ta’azzarar halin da ake ciki, da warware bambance-bambance ta hanyar gudanar da shawarwari.

Bugu da kari, sassan biyu sun amince da su nazarci kafuwar tsarin gudanar da hadin gwiwa, don ingiza alakar cinikayya da zuba jari, da ci gaba da amfani da tsarin na tattaunawa, da karfafa shawarwari, da tuntubar juna, da kyautata salon warware sabani, da fadada hadin gwiwa na zahiri, da ingiza alakar tattalin arziki da cinikayya mai dorewa, inganci da nagarta.

A ranakun Lahadi da jiya Litinin, bangarorin Sin da Amurka sun gudanar da tattaunawar kasuwanci a birnin Paris na Faransa. Yayin zantawar, wakilin musamman na kasar Sin kan harkokin cinikayya, kana mataimakin ministan kasuwancin kasar Li Chenggang ya bayyana cewa, a kwana daya da rabi, tawagogin bangarorin biyu sun gudanar da tattaunawa ta gaskiya kuma mai zurfi. Kana an cimma matsaya daya a matakin farko kan wasu batutuwa, kuma a mataki na gaba bangarorin biyu za su ci gaba da tafiyar da tsarin tattaunawar.

Li Chenggang ya ce, a wannan tattaunawa, bangarorin Sin da Amurka sun kara gane cewa, dangantakar ciniki cikin kwanciyar hankalin tsakanin kasashen biyu, tana amfanar da bangarorin biyu, har ma da duniya baki daya.

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

El-Rufai Ya Zargi ICPC Da DSS Kan Tsare Shi Ba Bisa Ƙa’ida Ba Da Neman Ya Yi Ritaya Daga Siyasa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.