ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagogin Sin Da Amurka Sun Zurfafa Tattaunawa Game Da Batutuwan Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Amurka

Tawagogin kasar Sin da na Amurka sun gudanar da tattaunawa mai zurfi da ma’ana, sun kuma yi musayar ra’ayoyi da shawarwari dangane da batutuwan tattalin arziki da cinikayya da kasashen biyu suke mayar da hankali a kansu, ciki har da tsare-tsaren harajin fito, da ingiza dangantakar cinikayya da zuba jari, tare da wanzar da sakamako na matakai da suka amincewa bayan tattaunawa.

Jagororin tattaunawar ta wannan karo da ta gudana a ranakun Lahadi da jiya Litinin, sun hada da jagoran tawagar Sin, kuma mataimakin firaministan kasar He Lifeng. Sai kuma bangaren Amurka da ya hada da sakataren baitul-malin kasar Scott Bessent, da wakilin cinikayyar Amurka Jamieson Greer.

Da yake tsokaci yayin sabon zagayen tattaunawar, He Lifeng ya ce, karkashin kyakkyawan tsari na muhimmiyar fahimtar juna tsakanin shugabannin kasashen biyu, da sakamakon zagaye biyar na tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da suka gudanar cikin shekarar da ta gabata, Sin da Amurka sun cimma jerin nasarori a fannonin raya tattalin arziki da na cinikayya.

ADVERTISEMENT

He ya ce, wadannan sakamako sun ingiza babban yanayi na tabbas, da daidaito cikin dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin sassan biyu, da ma tattalin arzikin duniya baki daya. Mataimakin firaministan na Sin ya kara da cewa, har kullum kasar Sin na adawa da matakin kakaba haraji daga bangare guda da Amurka ke aiwatarwa. Yana mai kira gare ta da ta kawar da dukkanin irin wadannan haraji, da ma sauran matakai masu haifar da tarnaki. A cewarsa, Sin za ta aiwatar da matakai na wajibi domin kare halastattun hakkoki da moriyarta.

Kazalika, Sin na fatan Amurka za ta rungumi tafarki na bai daya tare da Sin, ta kuma yi biyayya ga kudurorin musamman da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare da fadada fannonin hadin gwiwa, da takaita matsalolin da suke fuskanta, ta yadda hakan zai ingiza bunkasar alakar tattalin arziki, da cinikayya mai inganci da daidaito tsakanin kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

Wakilai daga bangaren Amurka kuwa, sun ce daidaito a yanayin alakar tattalin arziki, da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, na da matukar muhimmanci ga kasashen biyu da ma duniya baki daya, zai kuma tallafa matuka wajen bunkasa tattalin arzikin duniya, da samar da kariya ga tsarin rarraba hajoji zuwa sassan kasa da kasa, da daidaito ga hada-hadar kudade. Bangaren na Amurka, ya kuma bayyana bukatar magance takun-saka, da dakile kara ta’azzarar halin da ake ciki, da warware bambance-bambance ta hanyar gudanar da shawarwari.

Bugu da kari, sassan biyu sun amince da su nazarci kafuwar tsarin gudanar da hadin gwiwa, don ingiza alakar cinikayya da zuba jari, da ci gaba da amfani da tsarin na tattaunawa, da karfafa shawarwari, da tuntubar juna, da kyautata salon warware sabani, da fadada hadin gwiwa na zahiri, da ingiza alakar tattalin arziki da cinikayya mai dorewa, inganci da nagarta.

A ranakun Lahadi da jiya Litinin, bangarorin Sin da Amurka sun gudanar da tattaunawar kasuwanci a birnin Paris na Faransa. Yayin zantawar, wakilin musamman na kasar Sin kan harkokin cinikayya, kana mataimakin ministan kasuwancin kasar Li Chenggang ya bayyana cewa, a kwana daya da rabi, tawagogin bangarorin biyu sun gudanar da tattaunawa ta gaskiya kuma mai zurfi. Kana an cimma matsaya daya a matakin farko kan wasu batutuwa, kuma a mataki na gaba bangarorin biyu za su ci gaba da tafiyar da tsarin tattaunawar.

Li Chenggang ya ce, a wannan tattaunawa, bangarorin Sin da Amurka sun kara gane cewa, dangantakar ciniki cikin kwanciyar hankalin tsakanin kasashen biyu, tana amfanar da bangarorin biyu, har ma da duniya baki daya.

 

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • Sulaiman
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

MASU ALAKA

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
Daga Birnin Sin

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
Daga Birnin Sin

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Next Post
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

El-Rufai Ya Zargi ICPC Da DSS Kan Tsare Shi Ba Bisa Ƙa’ida Ba Da Neman Ya Yi Ritaya Daga Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.