ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

by Sulaiman and CGTN Hausa
44 minutes ago
Sin

Wani bincike kan ra’ayoyin jama’a da cibiyar bincike ta Pew ta kasar Amurka ta gudanar kwanan nan ya nuna cewa, idan aka kwatanta da sakamakon bincike da aka gudanar a shekarar 2024, yawan mutane masu goyon bayan kasar Amurka ya ragu a dukkan kasashen Najeriya, da Ghana, da Kenya, da Afirka ta Kudu, yayin da yawan mutanen da ke da ra’ayi mai kyau game da kasar Sin ke karuwa. Wannan sauyi ba kawai yake da alaka da bambancin manufofin hulda da kasashen waje na kasar Sin da na Amurka ba, har ma akwai nasaba da tattalin arziki, musamman ma fannin zuba jari.

Bisa wani rahoton da hukumar binciken yanayin tattalin arziki na kasar Amurka ko USBEA ta fitar a baya-bayan nan, zuwa karshen shekarar 2025, adadin kudin jari da kasar Amurka ta zuba wa nahiyar Afirka ya ragu zuwa dala biliyan 37.9, jimilla ce mafi kankanta tun daga shekarar 2008, wadda ta ragu da kaso 45.1% daga jimilla mafi yawa da aka samu a shekarar 2014. Yayin da alkaluma daga kasar Sin suka nuna cewa, tsakanin shekarar 2013 da ta 2024, jarin da kasar Sin ta zuba a kasashen Afirka kai tsaye ya yi ta samun karuwa, inda jimillar ta karu daga sama da dala biliyan 20 zuwa kimanin dala biliyan 43.8.

Bayan bambancin yawan jarin da Sin da Amurka suka zuba a nahiyar Afirka, bambancin kason jarin da suka kebe ma Afirka cikin dukkan kudin da suka zuba wa kasashen waje, shi ma abin lura ne. Bisa alkaluman da hukumar USBEA ta gabatar, cikin shekaru arba’in da suka gabata, kason kudin da Amurka ta zuba wa Afirka cikin dukkan jarin da kasar ta zuba a ketare, mafi yawa shi ne 2.57%, mafi kankanta kuma ya kasance 0.53%. Ta hakan za mu san cewa, ko da a lokacin da jimillar kudin da Amurka ta zuba ta kai matsayin koli, Afirka ba ta taba zama wata kasuwa mai muhimmanci a fannin zuba jari ga kasar Amurka ba. Sabanin haka, alkaluman da kasar Sin ta fitar sun nuna cewa, kasar ta fi nuna sha’awar zuba jari a kasashen Afirka. Misali, bisa alkaluman shekara ta 2025, jarin da kasar Sin ta zuba a Afirka ya kai kashi 4.45% na dukkan jarin da ta zuba wa kasashen ketare.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, wani bambanci mai muhimmanci da ya shafi hanyar da kasashen Sin da Amurka suke bi wajen zuba jari a nahiyar Afirka shi ne:A kasar Amurka, wasu manyan kamfanoni ne ke kula da aikin zuba jari a kasuwannin ketare, wadanda ke kokarin neman samun riba daga hawa da sauka na farashin albarkatun kasa a kasuwar duniya. Bisa tantance alkaluma na baya, za mu san cewa, yanayin karuwar jarin da Amurka ta zuba a kasashen Afirka ya samu ne tsakanin shekarar 2005 da ta 2014. A wancan lokacin, hauhawar farashin mai da na wasu danyun kayayyaki ta sa dimbin jari kwarara daga kasar Amurka zuwa sassan sarrafa mai, da iskar gas, da ma’adanai na Afirka. Duk da haka, da zarar farashin albarkatun kasa ya daina hauhawa, to, nan take ake fara samun janyewar jarin kamfanonin Amurka. Alkaluma sun nuna cewa, cikin yawan jarin Amurka da ya ragu a kasuwannin Afirka tsakanin shekarar 2014 da ta 2025, kaso 97% an janye shi ne daga bangaren hakar ma’adinai na kasashen Afirka.

Sabanin yadda kamfanonin Amurka ke son neman samun riba ta hanyar wasu damammaki na bangaren hada-hadar kudi, kamfanonin kasar Sin sun fi son kafa masana’antu, da tsarin sayar da kaya, da na samar da kayayyaki a kasashen Afirka, inda suke neman samun riba ta hanyar gudanar da ayyuka na dogon lokaci. Bugu da kari, jarin da kasar Sin ta zuba a Afirka ya shiga sana’o’i daban daban: daga gina ababen more rayuwa irinsu hanyoyin mota, da layin dogo, da tashoshin jiragen ruwa, da dai sauransu, zuwa ciniki da masana’antu masu alaka da wayoyin salula, da kayayyakin gida, da motoci, har ma da masana’antun zamani masu nasaba da sabon makamashi da fasahar kirkirarriyar basira ta AI, wadanda ke bunkasa cikin matukar sauri a ‘yan shekarun nan, sannan jari daga kasar Sin ya shafi kusan kowane fanni na masana’antu da bangaren sayayya na kasashen Afirka. A ganin kamfanonin kasar Sin, Afirka ba inda ake samun albarkatun kasa kawai ba ce, ita ma babbar kasuwa ce mai tasowa cikin sauri da ke da mutane biliyan 1.4, da ci gaban harkoki daban daban a dimbin biranenta.

LABARAI MASU NASABA

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Babu shakka, a tsakanin kasashen da ba sa nahiyar Afirka, wadanda manufofinsu suka fi biyan bukatun raya kasa da inganta rayuwar jama’a na kasashen Afirka za su fi samun karbuwa tsakanin ‘yan Afirka. Wannan wani muhimmin dalili ne da ya sa kasar Sin samun karin girmamawa da goyon baya daga ‘yan Afirka a ‘yan shekarun nan. (Bello Wang)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
  • Sulaiman
    Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

MASU ALAKA

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
Ra'ayi Riga

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Sin
Labarai

Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC

July 24, 2026

LABARAI MASU NASABA

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

July 24, 2026
Sin

Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC

July 24, 2026
Falalar Yawaita Istigifari (2)

Falalar Yawaita Istigifari (2)

July 24, 2026
Sin

Amurka Ta Kakaba Harajin Kaso 12.5% A Kan kayayyakin Nijeriya

July 24, 2026
Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.