Ana sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai shiga tsakani domin sasanta rikicin siyasa da ya kunno kai tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, da wasu gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin Jam’iyyar APC.
Rikicin ya ƙara tsananta ne bayan Gwamnonin APC, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC (PGF), Gwamnan Imo Hope Uzodimma, sun bayyana cewa ba za su goyi bayan wata ƙawance ko tsarin siyasa da zai raunana APC ko ’yan takararta a zaɓen 2027 ba.
Wannan matsaya ta zo ne yayin da Wike ke ƙarfafa shirin kawancen jam’iyyun mai taken “Rainbow Coalition”, wata ƙungiyar siyasa da ya ce manufarta ita ce tattara goyon bayan sake zaɓen Tinubu, ba tare da hana PDP da sauran jam’iyyun siyasa tsayar da ’yan takara a sauran kujerun zaɓe ba.
Wike ya kuma bayyana cewa goyon bayansa ga Tinubu ba yana nufin ya fice daga PDP ko kuma ya goyi bayan dukkan ’yan takarar APC ba. Ya ce yana da ’yancin tallafa wa ’yan takarar da ya zaɓa a sauran zaɓukan.
A cewar rahotannin siyasa, ana sa ran Tinubu zai gana da mambobin PGF bayan dawowarsa Nijeriya daga Turai domin tattauna matsalar da kuma neman hanyar sasanta ɓangarorin.
Wasu rahotanni sun kuma ce Wike, wanda ke Spain a halin yanzu, na iya ganawa da Tinubu a Faransa kafin Shugaban Ƙasar ya dawo Nijeriya.
Wike ya ce Shugaban Ƙasa yana sane da ayyukan “Rainbow Coalition” ɗinsa, yayin da gwamnonin APC ke ganin cewa irin wannan tsarin na iya haifar da rabuwar kai a tsakanin ’yan jam’iyyar da kuma ’yan takararta.
Rikicin ya zo ne yayin da jam’iyyun siyasa ke ƙara shirye-shiryen zaɓen 2027, musamman kan yadda za a haɗa goyon bayan siyasa ga takarar shugaban ƙasa da kuma ’yan takarar gwamna da ’yan majalisu a jihohi daban-daban.













