Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kashe mayaƙan Boko Haram da ISWAP 1,106 a Arewa maso Gabas cikin shekara guda.
Kwamandan Rundunar Operation Hadin Kai mai barin gado, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar ne, ya bayyana hakan yayin bikin miƙa ragamar rundunar ga sabon kwamanda, Manjo Janar Ibikunle Ajose, a Maiduguri.
Ya ce sojojin sun kuma ƙwato makamai sama da 475 da harsasai sama da 24,000, tare da lalata bama-bamai 295 da aka ƙera a cikin gida.
Rundunar ta kama mutane 758 da ake zargi da taimaka wa ’yan ta’adda wajen safarar makamai da sauran kayayyaki.
Haka kuma, mayaƙan JAS da ISWAP 969 da iyalansu sun miƙa wuya, yayin da aka ceto mutane 638.
Manjo Janar Abubakar ya ce ayyukan sojojin sun taimaka wajen mayar da iyalai sama da 7,000 da suka rasa matsugunansu zuwa garuruwansu a jihar Borno.
A nasa bangaren, sabon kwamandan rundunar, Manjo Janar Ibikunle Ajose, ya yi alƙawarin ci gaba da ayyukan da za su taimaka wajen dawo da zaman lafiya da inganta harkokin tattalin arziƙi a Arewa maso Gabas.














