Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya naɗa Barrister Hafsat Ada’u Kutama a matsayin mukaddashiyar shugabar Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta jihar (PCACC).
Mai ba Gwamnan shawara kan kafafen sada zumunta, Ibrahim Adam, ne ya sanar da naɗin a shafinsa na sada zumunta da aka tabbatar a ranar Laraba.
A cewar sanarwar, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Barrister Hafsat Ada’u Kutama domin ta jagoranci hukumar a matsayin mukaddashiyar shugaba har zuwa lokacin da za a samu cikakken shugaba bisa tsarin da ya dace.
Hukumar PCACC ita ce ke da alhakin karɓar korafe-korafen jama’a da kuma gudanar da bincike kan zarge-zargen cin hanci da rashawa da sauran abubuwan da suka shafi almundahana a jihar.
ADVERTISEMENT














