Memban ofishin siyasa na kwamitin koli na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan wajen kasar Wang Yi, ya gana da mataimakin firaminista, kana ministan wajen Pakistan Mohammad Ishaq Dar a jiya Alhamis a birnin New York na Amurka.Yayin ganawar, Wang Yi ya bayyana cewa, nasarar ziyarar firaministan Pakistan Muhammad Shahbaz Sharif a Sin, da kuma muhimmiyar sabuwar matsaya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, sun daukaka ginin al’umma mai makoma ta bai daya ta Sin da Pakistan zuwa wani sabon mataki.
Wang Yi ya ce Pakistan ta shiga babban taron kwamitin tsaro na MDD, da kuma taron “Rukunin abokan tsarin shugabancin duniya”, inda ta aika sako na farfado da iko da babban matsayin MDD, da kuma gyarawa da inganta tsarin shugabanci na duniya tare da dukkan bangarori.
Duk da matsayinta na mamba marar kujerar dindindin a kwamitin tsaron MDD, Pakistan ta dauki nauyin kiyaye zaman lafiya da tsaron duniya, kuma kasar Sin na jinjina mata kan hakan.
Wang Yi ya kara da cewa, shiga tattaunawar Amurka da Iran da Pakistan ta yi, ya nuna amincinta a matsayin mai shiga tsakani. Bugu da kari, Sin za ta ci gaba da tallafawa kokarin wanzar da zaman lafiya na Pakistan, tare da yin kira ga dukkan bangarorin da su rungumi tattaunawa, su inganta tsagaita bude wuta, da kuma gaggauta dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gulf na Gabas ta Tsakiya.
A nasa bangare, Dar ya gode wa Sin, saboda goyon bayan kokarin shiga tsakani na Pakistan, sannan ya bayyana cewa, shawara mai matakai biyar da Pakistan da Sin suka gabatar, domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gulf na Gabas ta Tsakiya, ya samu goyon baya daga bangarori daban daban. Kuma Pakistan za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen rage tashin hankali a yankin. (Safiyah Ma)















Discussion about this post