Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne ministan harkokin wajen kasar Mr. Wang Yi, ya halarci taron rukunin abokai na tsarin inganta jagorancin duniya, wato “Group of Friends of Global Governance” a jiya Alhamis a hedkwatar MDD da ke birnin New York, taron da ya hallara wakilan kasashe sama da 60, ciki har da ministocin harkokin wajen kasashen Pakistan, da Turkimenistan, da Cuba da Zimbabwe.
A jawabin da ya gabatar a gun taron, Wang Yi ya bayyana cewa, a watan Satumban bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta jagorancin duniya, wadda ta samu amincewa daga kasashe da kungiyoyin duniya kusan 160.
Daga nan kuma, bi da bi aka kafa rukunonin abokai na tsarin inganta jagorancin duniya a biranen New York, da Geneva da kuma Vienna, rukunonin da mambobinsu suka kai sama da 60.
Wang Yi ya jaddada cewa, domin inganta tsarin jagorancin duniya, kasar Sin ta gabatar da shawarar yin gyare-gyare ta wasu fannoni tara, wato na farko, a yi wa MDD garambawul don inganta ayyukanta. Na biyu, a inganta fada-a-ji na MDD da kuma kwarewarta. Na uku, a sa kaimi ga ayyukan kiyaye zaman lafiya su tafi tare da zamani. Na hudu, a hada kawunan kasa da kasa ta fannin gaggauta ci gaba. Na biyar, a dora ayyuka masu nasaba da hakkin dan Adam a kan tafarkin da ya dace. Na shida, a zurfafa gyare-gyaren tsarin tattalin arziki da hada-hadar kudi. Na bakwai, a kafa dokoki kan fasahar kirkirrariyar basira. Na takwas, a inganta ayyukan jagorantar harkoki masu alaka da yanar gizo da kuma sararin samaniya. Na tara, a inganta musayar al’adu da hakuri da juna da kuma koyi da juna.
Wang Yi ya kara da cewa, a lokacin kakan bana, kasar Sin za ta shirya taron dandalin tattauna harkokin inganta jagorancin duniya a birnin Xiong’an na kasar, kuma tana sa ran yin shawarwari tare da bangarori daban daban, game da yadda za a inganta tsarin jagorancin duniya. (Lubabatu Lei)















Discussion about this post