Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ta Kaya A Taron Matasan PDP Na Jihar Yobe

by
6 months ago
in Tambari
2 min read
Matasan
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela,

A taron farfado da hadin kan matasan jam’iyyar PDP a Gashuwa, shalkwatar karamar hukumar Bade da ke Jihar Yobe ya jawo cece-ku-ce tare da daga hankalin jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki. Yayin da wasu matasan suka fice zuwa PDP tare da bayyana dalilin daukar matakin da cewa sun yi hakan ne  zargin an yi watsi da su a jihar.

Wannan al’amarin ya gudana ne a wani taron karbar matasan a babban dakin taro da ke Gashuwa a karshen mako.

Labarai Masu Nasaba

Uwargidan Gwamnan Adamawa Ta Tallafa Wa Yara Mata Da Naira 200,000

2023: Bukola Saraki Kwararre Ne Wajen Shugabanci – Kawu Baraje

 

Daruruwan matasa suka halarci taron daga kananan hukumomin Yusufari, Nguru Karasuwa, Jakusko, Potiskum tare da samun wakilcin manyan jiga-jigan jam’iyyar PDP a Jihar Yobe irin su tsohon ministan ma’aikatar kula da harkokin ‘yan sanda, Alhaji Adamu Maina Waziri, tsohon dan takarar gwamna a jihar Yobe, Ambasada Iliya Damagum, tsohon dan takarar kujerar sanata a shiyyar gabashin Jihar Yobe, Hon. Abba Gana Tata da makamantan su.

A nasa bangaren, jami’in yada labarai na matasan jam’iyyar PDP a Inwar Lamar, Abubakar Sadik Abdullahi ya bukaci matasa a jihar da cewa lokaci ya yi wanda za su cire tsoro, su fito don kwatar yancinsu. Ya kara da cewa idan a baya an danne hakkokinsu, to yanzu jam’iyyar PDP ta share musu hawaye ta hanyar ba su cikikkiyar damar domin a dama da su a harkokin siyasa.

Sadik ya kara da cewa, matasa a Jihar Yobe a karkashin jam’iyyar PDP sun shirya tunkarar zabukan 2023 wajen ganin sun kwace mulki daga hannun APC tare da bayar da tabbacin samun goyon bayan jama’a.

 

Ita ma shugabar matan jam’iyyar PDP a karamar hukumar Bade, Fatima Muhammad Umar, ta bayyana cewa sun dauki dogon lokaci suna kokari wajen hada kan ‘ya’yan jam’iyyar don fuskantar alkibla daya tare da kauce wa abubuwan da za su kawo baraka da rabuwar kai a PDP.

 

Ta ce tunanin hakan ya zo ne biyo bayan la’akari da jiga-jigan jam’iyyar suka yi bisa wasu matsaloli da bambance-bambancen da aka sha fama da su a baya, wadanda suka kasance tarnaki a PDP, yayin da suka bayar da shawarar kirkiro da wani bangaren matasa maza da mata tare da sanya masa suna da: Inwar Lamar Matasan PDP, wanda ake sa ran zai shiga fadin jihohin kasar nan.

 

A nasa jawabinsa, shugaban matasan PDP a karamar hukumar Bade, Hon. Abdullahi Buba Katuzu, ya bayyana cewa matasa ne ‘yan gani-kashenin PDP suka shirya wannan taron domin hada kansu a yi tafiya mai tsabta a jam’iyyar. Ya ce wannan yana da nasaba da adalci da kulawa ta musamman da PDP ta bai wa matasa.

 

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan da kammala taron, Hon. Shariff Abdullahi, wanda ya wakilci Ambasada Iliya Damagum, ya ce, “Mun taru ne a wannan waje domin karfafa matasan jam’iyyar PDP.”

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gyaran Dokar Zabe: Me Ya Sa Cikin APC Da PDP Ya Duri Ruwa Da Tsarin ‘Yar Tinke?      

Next Post

Shugabancin Jam’iyya: APC Reshen Nasarawa Ta Yi Na’am Da Al-Makura

Labarai Masu Nasaba

Adamawa

Uwargidan Gwamnan Adamawa Ta Tallafa Wa Yara Mata Da Naira 200,000

by
5 months ago
0

...

Saraki

2023: Bukola Saraki Kwararre Ne Wajen Shugabanci – Kawu Baraje

by
5 months ago
0

...

Zabe

Gyaran Dokar Zabe: Me Ya Sa Cikin APC Da PDP Ya Duri Ruwa Da Tsarin ‘Yar Tinke?      

by
6 months ago
0

...

Nijeriya

Tutsun Da Aka Yi Wa Dimokuradiyyar Nijeriya Tun Daga Samun ‘Yancin Kai

by
8 months ago
0

...

Next Post
Almakura

Shugabancin Jam’iyya: APC Reshen Nasarawa Ta Yi Na’am Da Al-Makura

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: