A yau Asabar, kakakin ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya amsa tambayoyin da wasu kafofin yada labarai suka yi, dangane da muhawarar bangarorin Sin da Amurka a fannin tattalin arziki da cinikayya.
A cewar kakakin, bisa tattaunawar da bangarorin Sin da Amurka suka yi, Mista He Lifeng, mataimakin firaministan kasar Sin, zai jagoranci wata tawaga wajen gudanar da shawarwari tare da bangaren kasar Amurka, kan batutuwa masu nasaba da tattalin arziki da cinikayya, tsakanin yau 19 da 23 ga wata, a kasar Amurka. Kakakin ya kara da cewa, bangarorin Sin da Amurka za su yi muhawara bisa tushen matsaya daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma a baya.
Ban da haka, a kwanan baya, wasu kafofin yada labaru sun ba da labarin cewa, kungiyar kasashen Turai ta EU na fatan cewa kasar Sin za ta takaita fitar da motoci kirar kasar masu amfani da mabambantan makamashi zuwa kasashen Turai, sa’an nan idan kasar Sin ta ki daukar wannan mataki, to, za ta iya fuskantar karin harajin fito. Dangane da lamarin, kakakin ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya ce, wannan mataki na takaita fitar da kaya ya zama karya ka’idojin kungiyar ciniki ta duniya WTO, wanda kuma bai dace da al’adar kasuwanci, da ka’idar yin takara cikin adalci ba. Saboda haka kasar Sin ba za ta amince da shi ba.
Jami’in na kasar Sin ya kara da cewa, bangaren Sin bai taba sauya matsayinsa ba, wanda shi ne, dole a tabbatar da daidaiton moriyar kowa, da bin ka’idojin kungiyar WTO da dokokin kasashe daban daban, da kokarin kare moriyar kamfanonin Sin da na kasashen Turai, yayin da ake tsara dabarar daidaita sabanin ra’ayi tsakanin kasar Sin da kungiyar EU. (Bello Wang)














