ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

by Sulaiman
5 hours ago

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO

A kwanan baya, shugaban majalisar dokokin kasar Angola, Mista Adao Almeida, ya yi ziyarar aiki a kasar Sin. Yayin da yake hira da wakilin kafar CMG, Mista Almeida ya ce, kasar Sin tana da shugaba mai hangen nesa, wanda yake kulawa da al’ummar kasar cikin tsanake. A cewar Almeida, shugaba Xi Jinping na kasar Sin yana da wasu halaye na musamman, kamar dora matukar muhimmanci kan ci gaban tattalin arziki, da fahimtar ainihin kalubalolin da kasar Sin da sauran kasashe daban daban suke fuskanta, da kokarin neman bakin zaren warware matsalolin. 

A lokacin da ya ambaci shawarwari guda 4 da shugaba Xi ya gabatar a kokarin daidaita al’amuran duniya, Mista Almeida ya ce, wadannan shawarwari suna da amfani ga yunkurin kafa tsarin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, ta yadda za a samar da wani dandali na tattaunawa tsakanin kasashe daban daban, don tsara wasu ka’idoji na bai daya da za su biya bukatun daidaita al’amura, da ba da damar kara dora muhimmanci kan hadin kan al’ummun sassan duniya, maimakon kebabbun kasashe marasa alaka a tsakaninsu. 

Kana Mista Almeida ya bayyana kasar Sin a matsayin wata babbar kasa, wadda ke taka rawar gani a fannin zamanantar da al’umma, da sauya tsarin masana’antu zuwa na dijital. A cewarsa, dalilin da ya sa kasar Sin samun nasara a fannin raya kasa, shi ne tsarinta na siyasa mai inganci, da cikakken tunanin da ake da shi a fannin raya kasa, da yadda ake aiwatar da manufofi yadda ake bukata. Ban da haka, ingantaccen tsarin kasar na sanya ido kan harkoki daban daban, shi ma ya samar da gudunmowa sosai. 

ADVERTISEMENT

Har ila yau, Mista Almeida ya ambaci hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Sin da Angola ta fuskar tattalin arziki. Ya ce akwai daruruwan kamfanonin kasar Sin da suke aiwatar da harkokinsu a kasar Angola, wadanda suka zuba jari, gami da kafa rassa a kasar. Kana wasu daga cikinsu sun kwashe shekaru da dama suna kokarin raya harkokinsu a kasar Angola. Ban da haka, dimbin kamfanonin kasar Sin na taimaka wa kasar Angola a yunkurinta na raya sassa daban daban na tsarin tattalin arziki. (Bello Wang) 

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Shawarwari Tsakanin Sin Da Amurka Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Sulaiman
    Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

September 19, 2026
An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO

September 19, 2026
Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu
Daga Birnin Sin

Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu

September 18, 2026
Next Post
Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

September 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

September 19, 2026
Rikicin Fili: Harsashi Ya Yi Ajalin Ɗalibin Jami’a A Neja

Rikicin Fili: Harsashi Ya Yi Ajalin Ɗalibin Jami’a A Neja

September 19, 2026
An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO

An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO

September 19, 2026
Za A Gudanar Da Shawarwari Tsakanin Sin Da Amurka Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya

Za A Gudanar Da Shawarwari Tsakanin Sin Da Amurka Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya

September 19, 2026
Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

September 19, 2026
Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

September 19, 2026
2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

September 19, 2026
Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

September 19, 2026
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

September 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.