Wani ɗalibin mataki na 400 a Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBU), Lapai, Jihar Neja, Isma’il Ishaq Magaji, ya mutu bayan harsashin da ya yi ɓatan hanya ya same shi yayin rikicin fili.
Jami’ar ta ce lamarin ya faru ne a garinsu Wawa, da ke Ƙaramar Hukumar Borgu ta jihar Neja.
A wata sanarwa da jami’ar ta fitar ranar Asabar, Mataimakin Magatakardan jami’ar mai kula da yaɗa labarai, Baba Akote, ya ce Shugaban Jami’ar, Farfesa Mohammed Sulaiman, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin da abokansa.
Sulaiman ya bayyana mutuwar ɗalibin a matsayin babban rashi, inda ya yi kira ga al’ummar da ke cikin rikicin da su warware matsalolinsu ta hanyar tattaunawa tare da guje wa ƙarin tashin hankali.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, rundunar ’yansandan jihar ba ta tabbatar da faruwar lamarin ba.














