• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

by Leadership Hausa
1 year ago
Zargin

Kwamishiniyar Mata, Yara da Nakasassu ta Jihar Kano, Aisha Saji ta shiga tsakani kan wasu yara masu kankantar shekaru da ake zargin abokin mahaifinsu ya yi lalata da su domin tabbatar da adalci ga wadanda lamarin ya shafa.

Wata sanarwa da Daraktar Wayar da Kan Jama’a ta Ma’aikatar, Aishatu Haruna, wacce ta ba wa LEADERSHIP kwafinta, ta bayyana cewa kwamishiniyar ta dauki nauyin lamarin ne jim kadan bayan an yada labarin a wani shirin gidan rediyon ‘Yanchi da Rayuwa’.

  • An Samu Sabuwar Damar Kyautata Hulda Tsakanin Sin Da Hungary
  • Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

 Nan take Kwamishiniyar ta umurci daraktoci biyu da kwararrun ma’aikata da su tuntubi wadanda abin ya shafa tare da ba ta ra’ayi.

A cewar sanarwar, yayin ganawa da daya daga cikin wadanda abin ya shafa da mahaifiyarsa a ofishinta, kwamishiniyar ta nuna kaduwarta matuka da jin irin wannan mummunan aiki da aka aikata ga yaro dan shekara takwas da ya kai ga lalata masa dubura.

Bisa la’akari da halin da mutanen da lamarin ya shafa suka shiga, Saji ta yi alkawarin bin diddigin lamarin har zuwa karshe, sannan kuma ya yi kokarin ganin an samar da wata kafa ta gwamnati da za ta samu nasara a shari’a.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Ta kuma yi tayin biyan basussukan da aka tara na tsawon watanni ana jinyar wadanda abin ya shafa, wadanda har yanzu ba su samu cikakkiyar lafiya daga raunukan da suka samu na dubura ba, sannan ta kara tallafa wa dangin da kyautar tufafi da kudi da buhun shinkafa da masara.

Da take magana tun da farko, mahaifiyar wadanda lamarin ya shafa ta ce tsohon mijinta ne ya sanar da ita lamarin inda ya janye karar kuma ya lallashe ta da ta bar batun kai karar, amma ta yanke shawarar sake bude maganar shari’ar ta hanyar ‘yansanda, sannan ta kai kotu. An bayar da belin wadda ake zargin duk da hujjojin da likitan da ya bayar game da ‘ya’yanta.

Ta kuma kara da cewa, a wata ziyarar jinya, wani likita ya fitar da tsutsotsi da suka taru a duburarsu, ya yi wa yaran dinki a duburarsu lamarin da ya sanya shi zubar da hawaye yayin da dayan da abin ya shafa ya rika gudawa babu kakkautawa.

Sai dai mahaifiyar ta ce, duk da cewa an shigar da karar a gaban kotu, amma har yanzu ba a kira su gaban alkali ba.

A nasu jawabansu na daban, wadanda abin ya shafa ‘yan shekaru takwas zuwa goma sun ce wadanda ake zargin sun yi lalata da su ne ta hanyar yi musu barazanar cutar da su idan sun gaya wa wani irin cin zarafin da aka yi musu.

Sai dai sun bayyana cewa duk da wannan barazanar sun kai rahoton lamarin ga mahaifin nasu wanda ya bukaci su yi shiru tare da gargadar su da su boye maganar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

LABARAI MASU NASABA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.