• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

by Leadership Hausa
1 year ago
Zargin

Kwamishiniyar Mata, Yara da Nakasassu ta Jihar Kano, Aisha Saji ta shiga tsakani kan wasu yara masu kankantar shekaru da ake zargin abokin mahaifinsu ya yi lalata da su domin tabbatar da adalci ga wadanda lamarin ya shafa.

Wata sanarwa da Daraktar Wayar da Kan Jama’a ta Ma’aikatar, Aishatu Haruna, wacce ta ba wa LEADERSHIP kwafinta, ta bayyana cewa kwamishiniyar ta dauki nauyin lamarin ne jim kadan bayan an yada labarin a wani shirin gidan rediyon ‘Yanchi da Rayuwa’.

  • An Samu Sabuwar Damar Kyautata Hulda Tsakanin Sin Da Hungary
  • Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

 Nan take Kwamishiniyar ta umurci daraktoci biyu da kwararrun ma’aikata da su tuntubi wadanda abin ya shafa tare da ba ta ra’ayi.

A cewar sanarwar, yayin ganawa da daya daga cikin wadanda abin ya shafa da mahaifiyarsa a ofishinta, kwamishiniyar ta nuna kaduwarta matuka da jin irin wannan mummunan aiki da aka aikata ga yaro dan shekara takwas da ya kai ga lalata masa dubura.

Bisa la’akari da halin da mutanen da lamarin ya shafa suka shiga, Saji ta yi alkawarin bin diddigin lamarin har zuwa karshe, sannan kuma ya yi kokarin ganin an samar da wata kafa ta gwamnati da za ta samu nasara a shari’a.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Ta kuma yi tayin biyan basussukan da aka tara na tsawon watanni ana jinyar wadanda abin ya shafa, wadanda har yanzu ba su samu cikakkiyar lafiya daga raunukan da suka samu na dubura ba, sannan ta kara tallafa wa dangin da kyautar tufafi da kudi da buhun shinkafa da masara.

Da take magana tun da farko, mahaifiyar wadanda lamarin ya shafa ta ce tsohon mijinta ne ya sanar da ita lamarin inda ya janye karar kuma ya lallashe ta da ta bar batun kai karar, amma ta yanke shawarar sake bude maganar shari’ar ta hanyar ‘yansanda, sannan ta kai kotu. An bayar da belin wadda ake zargin duk da hujjojin da likitan da ya bayar game da ‘ya’yanta.

Ta kuma kara da cewa, a wata ziyarar jinya, wani likita ya fitar da tsutsotsi da suka taru a duburarsu, ya yi wa yaran dinki a duburarsu lamarin da ya sanya shi zubar da hawaye yayin da dayan da abin ya shafa ya rika gudawa babu kakkautawa.

Sai dai mahaifiyar ta ce, duk da cewa an shigar da karar a gaban kotu, amma har yanzu ba a kira su gaban alkali ba.

A nasu jawabansu na daban, wadanda abin ya shafa ‘yan shekaru takwas zuwa goma sun ce wadanda ake zargin sun yi lalata da su ne ta hanyar yi musu barazanar cutar da su idan sun gaya wa wani irin cin zarafin da aka yi musu.

Sai dai sun bayyana cewa duk da wannan barazanar sun kai rahoton lamarin ga mahaifin nasu wanda ya bukaci su yi shiru tare da gargadar su da su boye maganar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.