ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

by Sulaiman
34 minutes ago
Arewa

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewacin Nijeriya (NNGF) da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa sun sake jaddada aniyarsu ta magance matsalar rashin tsaro a yankin, inda suka bayyana goyon bayansu ga kafa rundunar ’yansandan jihohi tare da amincewa da wasu sabbin matakai domin magance tushen matsalolin tashin hankalin.

An bayyana hakan ne a cikin sanarwar bayan taron haɗin gwiwa da aka gudanar ranar Laraba a Gidan Sir Kashim Ibrahim da ke Kaduna, inda gwamnoni da sarakunan gargajiya suka yi nazari kan halin tsaron Arewacin Nijeriya.

Taron ya yaba wa Bola Ahmed Tinubu bisa ƙoƙarin da gwamnatinsa ke yi wajen magance matsalolin tsaron ƙasa, tare da yin alƙawarin ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro na tarayya ta hanyar inganta musayar bayanan sirri, ƙarfafa juriyar al’umma da kuma haɓaka haɗin gwiwar jihohin Arewa.

ADVERTISEMENT

Taron ya bayyana cewa idan aka horar da ’yansandan jihohi yadda ya kamata, aka tanade su da kayan aiki tare da ba su cikakken goyon baya, hakan zai taimaka matuƙa wajen yaƙi da rashin tsaro a faɗin ƙasar.

Taron ya kuma bayyana amincewarsa da sabon Kwamitin Amintattu na Gidauniyar Asusun tsaro ta Arewacin Nijeriya, tare da buƙatar mambobinsa su gudanar da aikinsu cikin adalci, gaskiya da ’yancin kai.

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

Gwamnonin sun yabawa jihohin da suka cika alƙawarinsu na bayar da gudummawar Naira biliyan ɗaya a kowane wata ga Asusun Tallafin Tsaro, suna mai cewa hakan alama ce ta haɗin kai da ɗaukar nauyin kare yankin baki ɗaya. Sun kuma yi kira ga sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula, kafafen yaɗa labarai da sauran al’umma su mara wa asusun baya.

Baya ga matakan tsaro, taron ya amince da ɗaukar matakan magance tushen matsalolin rashin tsaro, ciki har da talauci, rashin aikin yi, jahilci da yawaitar yara marasa zuwa makaranta. A saboda haka, ya yi alƙawarin ƙara zuba jari a fannonin ilimi, noma, ƙarfafa matasa, koyar da sana’o’i da samar da hanyoyin samun abin yi domin tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

Dangane da daminar bana, taron ya buƙaci gwamnatoci da hukumomin tsaro su tabbatar da tsaron manoma yayin aikin gona, tare da yin aiki tare da sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma domin hana rikice-rikicen da ka iya tasowa. Haka kuma, ya bayyana goyon bayansa ga bunƙasa kiwo da zamanantar da harkokin noma domin inganta rayuwar al’umma da bunƙasa tattalin arzikin yankin.

A ƙarshe, taron ya amince da faɗaɗa haɗin gwiwar jihohin Arewa zuwa sauran muhimman fannoni kamar ilimi, noma da lafiya, ta hanyar samar da tsari guda domin inganta ayyukan gwamnati da hanzarta ci gaban yankin.

Arewa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa
  • Sulaiman
    Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing
  • Sulaiman
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

MASU ALAKA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Labarai

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Next Post
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba - Adeyemi

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.