Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewacin Nijeriya (NNGF) da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa sun sake jaddada aniyarsu ta magance matsalar rashin tsaro a yankin, inda suka bayyana goyon bayansu ga kafa rundunar ’yansandan jihohi tare da amincewa da wasu sabbin matakai domin magance tushen matsalolin tashin hankalin.
An bayyana hakan ne a cikin sanarwar bayan taron haɗin gwiwa da aka gudanar ranar Laraba a Gidan Sir Kashim Ibrahim da ke Kaduna, inda gwamnoni da sarakunan gargajiya suka yi nazari kan halin tsaron Arewacin Nijeriya.
Taron ya yaba wa Bola Ahmed Tinubu bisa ƙoƙarin da gwamnatinsa ke yi wajen magance matsalolin tsaron ƙasa, tare da yin alƙawarin ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro na tarayya ta hanyar inganta musayar bayanan sirri, ƙarfafa juriyar al’umma da kuma haɓaka haɗin gwiwar jihohin Arewa.
Taron ya bayyana cewa idan aka horar da ’yansandan jihohi yadda ya kamata, aka tanade su da kayan aiki tare da ba su cikakken goyon baya, hakan zai taimaka matuƙa wajen yaƙi da rashin tsaro a faɗin ƙasar.
Taron ya kuma bayyana amincewarsa da sabon Kwamitin Amintattu na Gidauniyar Asusun tsaro ta Arewacin Nijeriya, tare da buƙatar mambobinsa su gudanar da aikinsu cikin adalci, gaskiya da ’yancin kai.
Gwamnonin sun yabawa jihohin da suka cika alƙawarinsu na bayar da gudummawar Naira biliyan ɗaya a kowane wata ga Asusun Tallafin Tsaro, suna mai cewa hakan alama ce ta haɗin kai da ɗaukar nauyin kare yankin baki ɗaya. Sun kuma yi kira ga sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula, kafafen yaɗa labarai da sauran al’umma su mara wa asusun baya.
Baya ga matakan tsaro, taron ya amince da ɗaukar matakan magance tushen matsalolin rashin tsaro, ciki har da talauci, rashin aikin yi, jahilci da yawaitar yara marasa zuwa makaranta. A saboda haka, ya yi alƙawarin ƙara zuba jari a fannonin ilimi, noma, ƙarfafa matasa, koyar da sana’o’i da samar da hanyoyin samun abin yi domin tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Dangane da daminar bana, taron ya buƙaci gwamnatoci da hukumomin tsaro su tabbatar da tsaron manoma yayin aikin gona, tare da yin aiki tare da sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma domin hana rikice-rikicen da ka iya tasowa. Haka kuma, ya bayyana goyon bayansa ga bunƙasa kiwo da zamanantar da harkokin noma domin inganta rayuwar al’umma da bunƙasa tattalin arzikin yankin.
A ƙarshe, taron ya amince da faɗaɗa haɗin gwiwar jihohin Arewa zuwa sauran muhimman fannoni kamar ilimi, noma da lafiya, ta hanyar samar da tsari guda domin inganta ayyukan gwamnati da hanzarta ci gaban yankin.














