ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

by Sadiq
32 minutes ago

Tsohon Darakta Janar na Hukumar Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC), Prince Mathew Adeniyi Adeyemi, ya musanta cewa ya taɓa ganawa da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ido da ido.

Adeyemi ya ce bincike mai zaman kansa ne kawai zai iya gano gaskiyar zargin da ke tattare da hukumar.

Ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta fitaccen mai amfani da Kafafen Sada Zumunta, Martins Vincent Otse, wanda aka fi sani da VeryDarkMan, inda ya ce ba zai iya tabbatarwa ko Gbajabiamila na da hannu a lamarin ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce bai taɓa yin ganawar sirri da Gbajabiamila ba, amma ya yi iƙirarin cewa ya yi magana da wani mutum da yake ganin shi ne Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasar sau uku ta waya ta hannun, Dolapo Tanimola.

Sai dai Adeyemi ya amince cewa ba zai iya tabbatar da cewa mutumin da ya yi magana da shi, shi ne Gbajabiamila ba, saboda ba su yi magana ta bidiyo ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

Lokacin da aka tambaye shi ko akwai yiwuwar Gbajabiamila ba shi da hannu a lamarin, Adeyemi ya amince da hakan, yana mai cewa ba shi da ikon cewa Shugaban Ma’aikatan ya yi ƙarya ko kuma ya faɗi gaskiya.

Ya ce wannan rashin tabbaci ne ya sa yake kira ga Shugaba Bola Tinubu da ya kafa bincike mai zaman kansa domin gano gaskiya.

A yanzu haka Adeyemi na fuskantar shari’a a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan zarge-zargen da suka shafi gudanar da PFIPC, wadda Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa babu ita.

Ana sa ran ci gaba da sauraron shari’ar a ranar 14 ga watan Yuli.

Taƙaddama ta ƙara ƙamari ne bayan Adeyemi ya zargi Gbajabiamila da neman kashi 48 cikin 100 na tallafin aiki na hukumar wanda ya kai Naira biliyan 27.4, da kuma karɓar Naira miliyan 400 da ya danganta da wasu naɗe-naɗe a hukumar.

Sai dai Gbajabiamila ya musanta zargin, yana cewa bai taɓa yin wata hulɗa da Adeyemi kai tsaye ko ta hannun wani ba, kuma ya yi barazanar ɗaukar matakin shari’a kan zargin.

A halin yanzu, Shugaba Bola Tinubu ya umarci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gabatar masa da rahoto cikin kwanaki 30.

Haka kuma Adeyemi ya bayyana cewa yana shirin miƙa kansa ga Rundunar ’Yansandan Nijeriya ko kuma Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS).

MASU ALAKA

Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa
Manyan Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.