Tsohon Darakta Janar na Hukumar Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC), Prince Mathew Adeniyi Adeyemi, ya musanta cewa ya taɓa ganawa da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ido da ido.
Adeyemi ya ce bincike mai zaman kansa ne kawai zai iya gano gaskiyar zargin da ke tattare da hukumar.
Ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta fitaccen mai amfani da Kafafen Sada Zumunta, Martins Vincent Otse, wanda aka fi sani da VeryDarkMan, inda ya ce ba zai iya tabbatarwa ko Gbajabiamila na da hannu a lamarin ba.
Ya ce bai taɓa yin ganawar sirri da Gbajabiamila ba, amma ya yi iƙirarin cewa ya yi magana da wani mutum da yake ganin shi ne Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasar sau uku ta waya ta hannun, Dolapo Tanimola.
Sai dai Adeyemi ya amince cewa ba zai iya tabbatar da cewa mutumin da ya yi magana da shi, shi ne Gbajabiamila ba, saboda ba su yi magana ta bidiyo ba.
Lokacin da aka tambaye shi ko akwai yiwuwar Gbajabiamila ba shi da hannu a lamarin, Adeyemi ya amince da hakan, yana mai cewa ba shi da ikon cewa Shugaban Ma’aikatan ya yi ƙarya ko kuma ya faɗi gaskiya.
Ya ce wannan rashin tabbaci ne ya sa yake kira ga Shugaba Bola Tinubu da ya kafa bincike mai zaman kansa domin gano gaskiya.
A yanzu haka Adeyemi na fuskantar shari’a a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan zarge-zargen da suka shafi gudanar da PFIPC, wadda Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa babu ita.
Ana sa ran ci gaba da sauraron shari’ar a ranar 14 ga watan Yuli.
Taƙaddama ta ƙara ƙamari ne bayan Adeyemi ya zargi Gbajabiamila da neman kashi 48 cikin 100 na tallafin aiki na hukumar wanda ya kai Naira biliyan 27.4, da kuma karɓar Naira miliyan 400 da ya danganta da wasu naɗe-naɗe a hukumar.
Sai dai Gbajabiamila ya musanta zargin, yana cewa bai taɓa yin wata hulɗa da Adeyemi kai tsaye ko ta hannun wani ba, kuma ya yi barazanar ɗaukar matakin shari’a kan zargin.
A halin yanzu, Shugaba Bola Tinubu ya umarci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gabatar masa da rahoto cikin kwanaki 30.
Haka kuma Adeyemi ya bayyana cewa yana shirin miƙa kansa ga Rundunar ’Yansandan Nijeriya ko kuma Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS).













