Majalisar Zartarwa ta Jihar Kaduna ta amince da sabbin matakai da za su inganta ilimi, noma, ababen more rayuwa da ci gaban tattalin arziƙi a faɗin jiha.
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ne ya sanar da hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan zaman Majalisar Zartarwa da aka gudanar a Kaduna.
Ya bayyana cewa daga cikin muhimman shawarwarin da majalisar ta amince da su akwai Manufar Ƙwarewar Rayuwa ta Jihar Kaduna (Kaduna State Life Skills Policy), wadda ta sanya Kaduna zama jiha ta farko a Nijeriya da ta samar da cikakkiyar manufa domin bai wa ɗalibai ilimi, ƙwarewa, ɗabi’u da ƙimomin da za su taimaka musu wajen samun nasara a makaranta, wurin aiki da kuma rayuwar yau da kullum.
A cewarsa, manufar za ta mayar da hankali kan inganta tsarin koyarwa da manhajar karatu, hanyoyin tantance ɗalibai, tare da ƙarfafa ƙwarewar malamai domin inganta ingancin ilimi a makarantun jihar.
Hakazalika, majalisar ta amince da Manufar Daidaito Tsakanin Mata da Maza a Fannin Ilimi, wadda ke da nufin tabbatar da daidaito wajen samun ilimi da kuma inganta sakamakon koyarwa da koyo a dukkan matakan ilimi.
A ɓangaren noma kuwa, majalisar ta amince da sayo tan 6,000 na takin zamani domin shirin noman shekarar 2026, a wani yunƙuri na ƙara yawan amfanin gona da tabbatar da wadatar abinci a jihar.
Haka kuma, majalisar ta amince da aiwatar da kashi na biyu na aikin gina titunan cikin gari guda 11 a ƙananan hukumomin Zariya da Sabon Gari, domin sauƙaƙa zirga-zirga, inganta kasuwanci da bunƙasa tattalin arziƙin yankunan.
Malam Ahmed Maiyaki ya ce dukkan waɗannan matakai na daga cikin ƙudirin gwamnatin Gwamna Sanata Uba Sani na aiwatar da manufofin da suka shafi rayuwar al’umma kai tsaye, ta hanyar bunƙasa jarin ɗan Adam, inganta rayuwar jama’a da kuma tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Kaduna.














