Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da ɗaga mafi ƙarancin kuɗin fansho zuwa Naira 20,000 a kowane wata ga masu ritaya na gwamnatin jiha da ƙananan hukumomi, daga Naira 12,000 da ake biya a baya, a wani yunƙuri na inganta jin daɗin masu karɓar fansho.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Sagir Musa, ne ya sanar da hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron Majalisar Zartarwa da Gwamnan Jihar, Umar Namadi, ya jagoranta.
Ya ce Gwamna Namadi ya amince da fara aiwatar da sabon tsarin biyan fanshon daga ranar 1 ga Yulin 2026.
A cewar kwamishinan, sake duba kuɗin fanshon na nuna ƙudirin gwamnatin jihar na inganta rayuwar ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya, domin girmama gudummawar da suka bayar wajen ci gaban Jihar Jigawa.
Domin tallafa wa aiwatar da sabon tsarin, Majalisar Zartarwar ta kuma amince da ware ƙarin Naira biliyan 2.068 a duk shekara ga Tsarin Fansho na Haɗin Gwiwa na Gwamnatin Jiha da Ƙananan Hukumomi.
Musa ya bayyana cewa ƙarin kuɗaɗen za su tabbatar da cikakken aiwatar da sabon mafi ƙarancin fansho tare da sauƙaƙa biyan haƙƙoƙin masu ritaya cikin lokaci.













