Dan takarar gwamnan Jihar Kaduna na jam’iyyar ADC, Isa Ashiru Kudan, ya bayyana cewa ya ziyarci tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, a Abuja.
Sai dai Ashiru bai bayyana takamaiman wurin da suka gana ba. Hakan na zuwa ne yayin da ya sha alwashin kawar da jam’iyyar APC daga mulki a zaɓen shekarar 2027.
Kafin hakan, Ashiru ya karɓi baƙuncin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kaduna ta Arewa kuma ɗan tsohon gwamnan, Bello El-Rufai.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook da aka tabbatar a ranar Talata bayan ganawarsa da El-Rufai, Ashiru ya bayyana tattaunawar tasu a matsayin mai amfani, yana mai cewa ta ƙara wa jam’iyyar ƙwarin gwiwa da azama gabanin zaɓen gwamnan jihar na shekarar 2027.
Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna ta shirya tsaf domin ƙalubalantar gwamnatin APC mai mulki, wadda ya zarga da gaza cika burin da al’ummar jihar suke da shi.














