A yau Talata, Bankin Duniya ya fitar da sabon rahoton tattalin arzikin kasar Sin a Beijing, inda ya bayyana cewa ci gaban tattalin arzikin kasar ta Sin ya ci gaba da dorewa duk da rashin daidaiton bangaren bukata da na samar da kayayyaki da kuma katsewar samar da makamashi a duniya.
Rahoton ya yi nuni da cewa, tattalin arzikin kasar Sin ya samu goyon baya daga zuba jari mai karfi a sashen manyan ayyukan fasaha da fitar da kayayyaki a farko-farkon shekarar 2026, inda ya kara da cewa tallafin sasashen manufofi, da zuba jari mai karfi a fannin manyan ayyukan fasaha da kuma ba da kariya daga tasirin katsewar samar da makamashi a duniya, sun taimaka wa daidaita bukatu na cikin gida a rubu’i na biyu na shekarar.
Kazalika, rahoton ya ce, an samu daidaito na hasashen koma-bayan da aka yi, yana mai nuni da cewa har a yanzu ana fuskantar barazanar sake samun koma-baya dangane da samar da makamashi a duniya da kuma farashin mai. (Abdulrazaq Yahuza Jere)













