Dakarun Rundubar Sojojin Nijeriya tare da jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) sun kama wasu mutane uku da ake zargin suna safarar miyagun ƙwayoyi ga ’yan ta’adda da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuka a Jihar Katsina.
An kama waɗanda ake zargin ne yayin wani samame na haɗin gwiwa da aka gudanar da misalin ƙarfe 5:15 na yammacin ranar Talata a ƙauyen Kagara da ke Ƙaramar Hukumar Kafur ta jihar, kamar yadda majiyoyin tsaro suka bayyana.
Aikin ya haɗa da dakarun Sansanin Soji na Gaba-gaba da ke Malumfashi da jami’an NDLEA na yankin Malumfashi, waɗanda suka gudanar da samamen bisa bayanan sirri da suka nuna wuraren da ake zargin ana rarraba miyagun ƙwayoyi a cikin al’ummar.
Masanin harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya wallafa a shafinsa na X cewa majiyoyi sun bayyana cewa manufar samamen ita ce katse hanyoyin da ake bi wajen kai miyagun ƙwayoyi da sauran abubuwan maye ga ƙungiyoyin masu aikata laifuka da ke aiki a yankin.
An bayyana sunayen waɗanda aka kama da Mohammed Lawan mai shekara 34, Muhawiya Haruna mai shekara 40, da Junadata Usman mai shekara 40.













