ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Marubuta Ta Alƙalam Za Ta Yi Taron Tunawa Da Mahmoon Baba-Ahmed

by Sulaiman
3 years ago
Mahmoon Baba-Ahmed

Ƙungiyar Marubuta Alƙalam da ke Kaduna ta bayyana cewa za ta shirya taron tunawa da uban ƙungiyar kuma gwarzon ɗan kishin ƙasa ɗin nan, Alhaji Mahmoon Baba-Ahmed, wanda Allah ya yi wa rasuwa shekaru biyar da su ka gabata.

Shugabar ƙungiyar, Hajiya Halima Abdullahi K/Mashi, ta bayyana a cikin wata takarda ga manema labarai cewa za a yi taron a Gidan Arewa da ke Kaduna a ranar Alhamis, 9 ga Fabrairu, 2023, wadda ta yi daidai da shekaru biyar cur da rasuwar marubucin.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Raba Auren ‘Yar Ganduje Da Mijintap

Alhaji Mahmoon ya rasu ne a Kaduna a ranar Alhamis, 9 ga Fabrairu, 2018, ya na da shekaru 77 a duniya.

ADVERTISEMENT

Mahmoon Baba-Ahmed sanannen ɗan jarida ne kuma marubuci wanda ya yi fice a aikin rediyo a matsayin wakilin gidan Rediyon Nijeriya na Kaduna a jihohi da dama. Daga bisani ya riƙe muƙamai da su ka haɗa da Shugaban gidan Rediyon Kano da Manajan Daraktan Hukumar Yaɗa Labarai ta Jihar Kaduna (KSMC).

Haka kuma ya kasance mai sharhi kan al’amurran yau da kullum a filayen musamman da aka ware masa a jaridu da su ka haɗa da Triumph, Blueprint da Aminiya, da kuma gidajen talabijin na DITV da Liberty da gidan rediyo na Alheri da na Liberty.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Marigayi Mahmoon ya rubuta littattafan adabi guda shida a rayuwar sa waɗanda su ka haɗa da littafin waƙe mai suna ‘Ɗan Hausa’, da littattafan wasan kwaikwayo guda biyu (‘Uwani Reza’ da ”Yar Halas’), da fassarar littattafai uku na mashahurin marubucin nan na ƙasar Ingila, wato William Shakespeare.

Littattafan Shakespeare da ya fassara su ne: ‘Macbeth’ (‘Makau’), ‘Julius Caesar’ (‘Jarmai Ziza’), da ‘Romeo and Juliet’ (‘Habiba Ta Habibu’).

Takardar sanarwar ta ce ɗaya daga cikin abubuwan ban-sha’awa da za a gudanar a taron shi ne gabatar da littafin ƙarshe da Mahmoon ya rubuta, wato ‘Habiba Ta Habibu’, wanda shi kaɗai ne marigayin bai samu bugawa ba har ya rasu, amma an buga shi a bana.

Hajiya Halima ta kuma bayyana cewa Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, shi ne babban baƙo na musamman a taron, yayin da Shugaban gidan talabijin da rediyo na Liberty, Dakta Ahmed Tijjani Ramalan, shi ne shugaban taron.

Bugu da ƙari, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli, zai kasance uban taron, yayin da tsohon Shugaban Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Tarayya, Mai Shari’a Umaru Abdullahi (Walin Hausa), shi ne babban baƙo na musamman.

Ta ce Shugaban Shiyyar Kaduna ta hukumar Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Alhaji Buhari Auwalu, shi ne babban baƙo mai jawabi, sannan babban malami a Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Adamu Ibrahim Malumfashi, zai yi sharhi kan littattafan marigayin.

A cewar shugabar ƙungiyar, manufar taron ita ce a tuno da muhimman ayyukan kishin ƙasa da Alhaji Mahmoon yayi, tare da ƙara kwaɗaita wa jama’a muhimmancin sambarka ga magabatan mu da su ka ba da gudunmawa ga cigaban ƙasa ta hanyoyin da Allah hore masu.

Ta ce za kuma a yi amfani da wannan damar a karrama wasu ‘ya’yan ƙungiyar ta Alƙalam waɗanda su ka riga mu gidan gaskiya.

Mahmoon Baba-Ahmed
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Gini Ya Rufta, Ya Kashe Mutane, Da Dama Sun Jikkata A Abuja

Gini Ya Rufta, Ya Kashe Mutane, Da Dama Sun Jikkata A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.