Sakatare janar na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban kasar Xi Jinping ya ba da muhimmin umurni kan ayyukan rigakafin ambaliyar ruwa da karfafa ceton jama’a a kasar.
Xi Jinping, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin aikin soja na tsakiya ya nuna cewa, a kwanakin baya-bayan nan, an samu rushewar madatsun ruwa da zaftarewar kasa a jere a yankunan Guangxi, Hubei da Gansu na kasar sakamakon ruwan sama da iska mai karfi, lamarin da ya janyo hasarar rayuka da jikkatar jama’a, tare da asarar dukiya mai dimbin yawa.
Dole ne a yi duk mai yiwuwa don gudanar da ayyukan ceto, da na ba da jinya ga wadanda suka jikkata, da kuma tsugunar da jama’ar da abin ya shafa, ta yadda za a rage yawan asarar rayuka da raunuka gwargwadon karfi, tare da rigakafin sake aukuwar barnar da bala’in ya haifar.
Xi Jinping ya jaddada cewa, kamata ya yi dukkannin yankuna da hukumomin da abin ya shafa su dage kan aiwatar da matakan da aka riga aka tsara, da zurfafa bincike da kawar da abubuwa masu haifar da hadari a koguna, tafkuna, madatsun ruwa, da wuraren da ake yawan samun abkuwar bala’o’in, da kuma karfafa aikin sa ido da fadakarwa, da shirye-shiryen ceto da agaji na gaggawa, kana da aiwatar da dukkan ayyukan rigakafi da magance bala’o’i daban daban yadda ya kamata, domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.
Sannan, firaministan kasar Sin Li Qiang ya yi nuni bisa ga umurnin cewa, saboda yawaitar fadawa cikin yanayi mai tsanani a baya-bayan nan, ya kamata ofishin kula da rigakafin ambaliyar ruwa da fari na kasa, da ofishin rage hadurra da ba da agaji na kasa su jagoranci yankuna daban-daban wajen sanya ido sosai kan yanayin ruwan sama da ambaliyar ruwa, da karfafa sa-ido da fadakarwa game da hadurra, da kuma yin duk mai yiwuwa wajen gudanar da aikin ceto da ba da agaji. (Bilkisu Xin)













