Rundunar ’Yansandan Jihar Legas ta kama mutane 150 da ake zargi da aikata laifuka yayin wani samame da ta kai maboyar masu laifi a yankunan Igando da Idimu, a wani ɓangare na ci gaba da yaƙin da take yi da aikata laifuka a faɗin jihar.
An gudanar da samamen ne da sanyin safiyar ranar Lahadi ƙarƙashin aikin Operation KO S’AYE, bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan wasu da ake zargin ’yan daba ne da ke addabar yankin Area M.
Mai magana da yawun rundunar, Abimbola Adebisi, ya ce jami’an ’yansanda daga sassa daban-daban na rundunar sun kai samame maboyar masu laifi da ke Boolar, tashar mota ta Okofilling da ke Igando, da sauran wuraren da aka gano a matsayin mafakar masu laifi, domin fatattakar masu aikata laifuka da kuma tabbatar da tsaron jama’a.
A yayin samamen, jami’an ’yansanda sun ƙwato bindiga kirar dobul-barel guda ɗaya, bindigogi kirar singul-barel guda biyu, wata gajeriyar bindiga ƙirar dobul-barel da aka ƙera a gida, babura 100 marasa rajista, wayoyin hannu 54, kayan sojoji guda biyu, injinan janareta shida da ake zargin an sace su ne, tsafe-tsafe iri-iri, da kuma wasu abubuwan da ake zargin tabar wiwi ce da sauran miyagun ƙwayoyi.













