Game da zargi da wasu gwamnatocin kasashe da dama suka yi, kan gwajin harba makamai masu linzami da kasar Sin ta gudanar, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Talata 7 ga wannan wata, cewa wannan gwaji aikin horarwa ne na sojojin kasar Sin, don haka bai dace kasashen da abin ya shafa su dauki wannan batu da wata ma’ana ba.
Mao Ning, ta yi nuni da cewa, gwajin ba a nufi wata kasa da shi ba. Kuma Sin ta riga ta sanar da tsibiran Solomon, da sauran kasashen yankin kudancin tekun Pasifik da abin ya shafa, wanda hakan ya dace da dokoki da ka’idojin kasa da kasa.
Game da girgizar kasa da ta abku a kasar Venezuela, Mao Ning ta ce, kasar Sin ta maida hankali kan bala’in, kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sako ga shugabar wucin gadi ta kasar Delcy Rodríguez, cewa gwamnatin Sin za ta kara samar da gudummawa da kimarta ta kai Yuan miliyan 100, ban da gudummawar da Sin ta riga ta bayar ga Venezuela kafin hakan.
Kana kungiyar Red Cross ta kasar Sin, ta gaggauta samar da kudi har dalar Amurka dubu 300 ga kungiyar Red Cross ta Venezuela. Kasar Sin tana son ci gaba da samar da goyon baya ga Venezuela bisa yanayin bala’in da ya auku a kasar. (Zainab Zhang)














