A bana ake cika shekaru 30 tun bayan da kasar Sin ta rattaba hannu kan yarjejeniyar MDD ta kare dokar teku ko UNCLOS. A cewar kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce kulla yarjejeniyar, da fara aiwatar da ita jigo ne na wanzar da gaskiya da adalci a odar teku tsakanin kasa da kasa, da kara karfafa tsarin jagorancin duniya bisa adalci da daidaito.
Mao, wadda ta bayyana haka a Talatar nan, ta ce cikin shekaru 30 da suka shude, Sin ta aiwatar da hakkokinta, ta sauke nauyin dake wuyanta karkashin yarjejeniyar bisa sahihanci. Kazalika, Sin ta kasance mai ingiza ruhin cudanyar sassa mabambanta da ke kunshe cikin yarjejeniyar, da goyon bayan ayyukan cibiyoyi uku na kasa da kasa da aka kafa bisa tanadin yarjejeniyar ta UNCLOS.
Har ila yau, ta yi aiki tare da wasu sassa da dama wajen kare kwanciyar hankali da tsaro a kan teku, da ingiza ci gaba mai dorewa a teku, da karfafa binciken kimiyya a teku, da kare muhalli, da ingiza musaya da hadin gwiwa a harkokin teku. Karkashin wadannan yunkuri, Sin ta taka rawar gani a fannin inganta tsarin jagorancin harkokin teku, da bunkasa walwalar dukkanin bil’adama. (Saminu Alhassan)














