Majalisar Dattawan Nijeriya ta bayyana matuƙar damuwa kan tabarbarewar harkokin tsaro a ƙasar, tana mai gargaɗin cewa sacewa da kashe tsofaffin jami’an soji da ’yan ta’adda ke yi na nuna wani sabon mataki mai haɗari na matsalar tsaro a Nijeriya.
Majalisar ta ce yawaitar hare-haren da ake kai wa jami’an soji masu aiki da waɗanda suka yi ritaya na barazana ga zaman lafiyar ƙasa, amincewar jama’a da kuma tsarin tsaron Nijeriya.
Wannan damuwar ta biyo bayan wani ƙuduri da Abdulaziz Yar’Adua ya gabatar a zaman majalisar, kan rasuwar tsohon Janar na Soji, Alkali Abubakar, wanda aka yi garkuwa da shi tare da matarsa a Jihar Katsina a ranar 30 ga Mayu, 2026, kafin daga bisani ya rasu a hannun masu garkuwa da shi.
Bayan amincewa da ƙudurin, sanatoci sun yi tsayuwar minti ɗaya domin girmama marigayin, tare da yanke shawarar miƙa saƙon ta’aziyyarsu ga iyalansa da kuma Rundunar Sojin Nijeriya.













