• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Matsaloli Na Barazana Ga Kawancen Jam’iyyun Adawa 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Adawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da kotun koli ta zartar da hukunci na tabbatar da nasarar Shugaban kasa, Bola Tinubu a zaben 2023, jam’iyyun adawa sun yi kunkurin shirya kawance domin tunkarar APC a 2027, sai dai kuma matsaloli sun turnuke wannan yukurin na jam’iyyun adawa. 

Amma tambayoyin mai muhimmanci da mutane ke ci gaba da yi ita ce, yadda jam’iyyun adawan za su samu nasarar yin wannan kwance bayan da sun gaza magance matsaloli da yawa kan lamarin.

  • Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023
  • Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

Jiga-jigan ‘yan siyasa a tsakanin jam’iyyun adawa sun ci gaba da tattaunawa tare da shawartar juna kan kafa kwancen siyasa ta yadda za su sami karfin tunkarar Shugaba Tinubu wanda zai nemi wa’adin mulki na biyu bayan shudewar mulkinsa na farko a 2027.

Idan za a iya tunawa dai, an samu irin wannan kwancen siyasa a 2013 lokacin da jam’iyyun CPC, ACN, ANPP, APGA da kuma wani bangare na jam’iyyar PDP suka dunkule wuri daya tare da samar da jam’iyya daya mai suna APC.

Tun a ranar 15 ga Oktoban 2023, dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar ya yi kira ga daukacin jam’iyyun adawa da ke kasar nan wajen samar da kwancen siyasa domin takatar da APC na yunkurin mayar da Nijeriya karkashin jam’iyya daya. Ya dai bayyana hakan ne lokacin da yake amsar bakwancin mambobin kwamitin zartarwa na cibiyar hadakar jam’iyyu.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ya ce, “Muna ganin yadda jam’iyyar APC tane kara kaimi wajen mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya. Idan har muka kasa hada kai wajen kalubantar jam’iyya mai mulki, za ta lalata mana dimokuradiyya kuma hakan zai shafi goben yaran da za a haifa nan gaba.”

Bayan haka, jam’iyyun PDP, NNPP, ADC, APM, SDP, YPP, da ZLP sun kafa wata kungiya da suka kira da CCPP bayan ganawa da shugabannin jam’iyyun guda 7 da ya gudana a shalkwatan jam’iyyar SDP da ke Abuja a ranar 6 ga Disambar 2023.

Shugabannin jam’iyyun adawa na ci gaba da sokar gwamnatin Tinubu na cewa ya kawo wasu tsare-tsaren tattalin arziki da suka janyo tsadar rayuwa da fatara da kuma radadin kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Haka kuma sun bayyana damuwarsu kan karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Sai dai kuma sakataren jam’iyyar APC na kasa, Felid Morka, ya bukaci ‘yan Nijeriya kar su dauki kawacen jam’iyyun adawa da muhimmanci, su kaance da jam’iyyar APC.

Bincike ya tabbatar da cewa har yanzu ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyya daban-daban da masu ruwa da tsaki na jam’iyyun adawa ba su kammala amincewa da wannan kawancin ba tare da kin yin watsi da akidar jam’iyyunsu. Haka kuma ba su yarda da yi wa wata sabuwar jam’iyya rajista ba.

An bayyana cewa kafin kawancen jam’iyyun adawan ya yuwu, sai dukkan jam’iyyun sun bayar da takardunsu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kafin su samu damar yi wa sabon jam’iyya rajista.

Ana ganin cewa wannan kawancen na jam’iyyun adawa zai yi wuya saboda akwai bambance-bambancin ra’ayoyi a tsakanin mambobin jam’iyyun.

Masu bincike sun bayana cewa matsalolin da ke barazana ga dorewar kawancen dai sun hada da rikicin cikin gina da rabuwar kai a tsakanin manyan jam’iyyun adawa. Sun kuma bayyana cewa za a samu matsala wajen fitar da dan takara idan har aka samu nasarar yin wannan kawance.

Haka kuma suna ganin cewa wasu manyan ‘yan siyasa masu matukar karfi da ke cikin gwamnatin Tinubu ba za su taba bari wannan kawanci ya samu nasara ba, domin kalubalantarsa a 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kabilanci Da Magudin Zabe Ke Kassara Samun Shugabanci Nagari – Jonathan

Next Post

Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

6 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.