• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Matsaloli Na Barazana Ga Kawancen Jam’iyyun Adawa 

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Adawa

Bayan da kotun koli ta zartar da hukunci na tabbatar da nasarar Shugaban kasa, Bola Tinubu a zaben 2023, jam’iyyun adawa sun yi kunkurin shirya kawance domin tunkarar APC a 2027, sai dai kuma matsaloli sun turnuke wannan yukurin na jam’iyyun adawa. 

Amma tambayoyin mai muhimmanci da mutane ke ci gaba da yi ita ce, yadda jam’iyyun adawan za su samu nasarar yin wannan kwance bayan da sun gaza magance matsaloli da yawa kan lamarin.

  • Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023
  • Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

Jiga-jigan ‘yan siyasa a tsakanin jam’iyyun adawa sun ci gaba da tattaunawa tare da shawartar juna kan kafa kwancen siyasa ta yadda za su sami karfin tunkarar Shugaba Tinubu wanda zai nemi wa’adin mulki na biyu bayan shudewar mulkinsa na farko a 2027.

Idan za a iya tunawa dai, an samu irin wannan kwancen siyasa a 2013 lokacin da jam’iyyun CPC, ACN, ANPP, APGA da kuma wani bangare na jam’iyyar PDP suka dunkule wuri daya tare da samar da jam’iyya daya mai suna APC.

Tun a ranar 15 ga Oktoban 2023, dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar ya yi kira ga daukacin jam’iyyun adawa da ke kasar nan wajen samar da kwancen siyasa domin takatar da APC na yunkurin mayar da Nijeriya karkashin jam’iyya daya. Ya dai bayyana hakan ne lokacin da yake amsar bakwancin mambobin kwamitin zartarwa na cibiyar hadakar jam’iyyu.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Ya ce, “Muna ganin yadda jam’iyyar APC tane kara kaimi wajen mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya. Idan har muka kasa hada kai wajen kalubantar jam’iyya mai mulki, za ta lalata mana dimokuradiyya kuma hakan zai shafi goben yaran da za a haifa nan gaba.”

Bayan haka, jam’iyyun PDP, NNPP, ADC, APM, SDP, YPP, da ZLP sun kafa wata kungiya da suka kira da CCPP bayan ganawa da shugabannin jam’iyyun guda 7 da ya gudana a shalkwatan jam’iyyar SDP da ke Abuja a ranar 6 ga Disambar 2023.

Shugabannin jam’iyyun adawa na ci gaba da sokar gwamnatin Tinubu na cewa ya kawo wasu tsare-tsaren tattalin arziki da suka janyo tsadar rayuwa da fatara da kuma radadin kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Haka kuma sun bayyana damuwarsu kan karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Sai dai kuma sakataren jam’iyyar APC na kasa, Felid Morka, ya bukaci ‘yan Nijeriya kar su dauki kawacen jam’iyyun adawa da muhimmanci, su kaance da jam’iyyar APC.

Bincike ya tabbatar da cewa har yanzu ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyya daban-daban da masu ruwa da tsaki na jam’iyyun adawa ba su kammala amincewa da wannan kawancin ba tare da kin yin watsi da akidar jam’iyyunsu. Haka kuma ba su yarda da yi wa wata sabuwar jam’iyya rajista ba.

An bayyana cewa kafin kawancen jam’iyyun adawan ya yuwu, sai dukkan jam’iyyun sun bayar da takardunsu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kafin su samu damar yi wa sabon jam’iyya rajista.

Ana ganin cewa wannan kawancen na jam’iyyun adawa zai yi wuya saboda akwai bambance-bambancin ra’ayoyi a tsakanin mambobin jam’iyyun.

Masu bincike sun bayana cewa matsalolin da ke barazana ga dorewar kawancen dai sun hada da rikicin cikin gina da rabuwar kai a tsakanin manyan jam’iyyun adawa. Sun kuma bayyana cewa za a samu matsala wajen fitar da dan takara idan har aka samu nasarar yin wannan kawance.

Haka kuma suna ganin cewa wasu manyan ‘yan siyasa masu matukar karfi da ke cikin gwamnatin Tinubu ba za su taba bari wannan kawanci ya samu nasara ba, domin kalubalantarsa a 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version