Ɗan Majalisar Tarayya, Abdulmumin Jibrin, ya bayyana ƙwarin gwiwarsa cewa Shugaba Bola Tinubu zai lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027 a Kano, duk da tasirin siyasar tsohon Gwamnan jihar, Rabiu Musa Kwankwaso.
Kofa, wanda ke wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji, ya bayyana hakan ne a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels a ranar Laraba, yayin da yake magana kan siyasar Kano gabanin zaɓen 2027.
Kwankwaso, wanda ya mulki Kano sau biyu, zai yi takarar shugaban ƙasa na 2027 a matsayin abokin takarar Peter Obi a ƙarƙashin jam’iyyar NDC.
A baya Kofa ya kasance cikin tsarin tafiyar Kwankwasiyya, amma ya ce ya san tsarin siyasar ɗariƙar sosai, kuma yana da yaƙinin cewa APC za ta iya kayar da ita.
“Wa ya fi mu sanin Kwankwasiyya? Mun san dukkanin tsarin siyasarsu,” in ji Kofa, yayin da yake bayar da tabbacin APC za ta lashe wa Tinubu Kano.
Ya ce bai kamata a rikita ra’ayoyin jama’a da abin da zai faru a zaɓe ba, domin sakamakon zaɓen ne zai nuna ainihin matsayar masu kaɗa ƙuri’a.
Kofa, ya kuma ce jaddada cewar masu goyon bayan Tinubu sun ƙaru a yankin Arewa.
Ya ce manyan jiga-jigan APC a Kano suna aiki tare kuma suna shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.
Kalaman Kofa na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ’yan siyasa da jam’iyyu ke ƙara shirye-shiryen tunkarar zaɓen shugaban ƙasa na 2027, yayin da Tinubu ke neman wa’adi na biyu.













