ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 weeks ago
Adamawa

Bayan kasa da awanni 24 da gwamnatin Jihar Adamawa ta rufe makarantun kwana, ‘yansanda sun kama masu satar mutane uku a jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar a Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana cewa kamun ya biyo bayan korafi da aka samu a ranar 19 ga Nuwamba, 2025, daga wani mazaunin wani kauye a Karamar Hukumar Song, cewa a ranar 18 ga Nuwamba, 2025, ya samu kiran waya ta barazana daga wani da ba a san ko waye ba.

  • Dogaro Da Noman Gargajiya Kadai Ba Zai Iya Wadatar Da  Nijeriya Ba – Farfesa Rabi’u
  • Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka

A cewar sanarwar, mai kiran waya ya nemi a biya shi Naira miliyan 2 ko kuma a yi garkuwa da shi har ma da yiwuwar a kashe shi.

ADVERTISEMENT

“Bayan karbar korafin, kwamishinan ‘yansanda, Dankombo Morris, ya umurci Mataimakin Kwamishinan ‘Yansanda na Sashen Bincike na Jiha, Yola, da ya gudanar da bincike tare da tabbatar da kama masu laifin,” in ji shi.

Mutanen da aka kama su ne Ahmadu Alhaji Halilu, mai shekara 24; Adamu Buba Balejo, mai shekara 21; da Hassan Alhaji Liman, duk maza daga Gundumar Malabu a Karamar Hukumar Fufore.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Babban Mai Sayar Da Miyagun Kwayoyi Ga ‘Yan Ta’adda Na Boko Haram

NDLEA Ta Kama Ƙwayar Tiramadol 396,000 A Filin Jirgin Saman Yola

“Yayin binciken, wadannan mutum uku sun amsa laifinsu. An kuma samu katin SIM da aka yi amfani da shi wajen aikata laifin, wanda za a dauka a matsayin hujja.”

Kwamandan ‘yansanda, wanda ya yaba wa jami’an da suka shiga aikin, ya tabbatar da jajircewar rundunar wajen ganowa da kama, da gurfanar da masu laifi a fadin jihar.

Gwamnatin Jihar Adamawa ta rufe dukkan makarantun kwana na gwamnati da masu zaman kansu a jihar a ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan Ilimi da Ci gaban Dan’Adam, Dr Umar Pella, ya sanyawa hannu, an bayyana cewa matakin Fintiri na rufe makarantun kwana yana nufin kauce wa faruwar irin sace dalibai da aka yi a Jihohin Neja da Kebbi.

“Dangane da kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta a yanzu, musamman abin da ya faru da dalibai a Jihohin Neja da Kebbi, an lura da takaici cewa makasudin masu laifi su ne makarantun sakandire na kwana.

“Idan aka yi la’akari da wannan mummunan yanayi a kasar, Mai Girma Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya umarce ni da in rufe dukkan makarantun kwana a fadin jihar, ko makarantu na gwamnati ne ko masu zaman kansu.”

Ya kara da cewa, “Dukansu su kasance makarantun jeka da ka dawo a halin yanzu. Saboda haka, ta wannan wasika, dukkan shugabanni da masu mallakar makarantu na gwamnati da na masu zaman kansu su mayar da dalibansu jeka ka dawo.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas
Tsaro

Sojoji Sun Kama Babban Mai Sayar Da Miyagun Kwayoyi Ga ‘Yan Ta’adda Na Boko Haram

November 21, 2025
NDLEA
Tsaro

NDLEA Ta Kama Ƙwayar Tiramadol 396,000 A Filin Jirgin Saman Yola

November 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Next Post
Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano

Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.